< Irmiya 39 >

1 A shekara ta tara ta Zedekiya sarkin Yahuda, a wata na goma, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fita yaƙi da Urushalima da dukan sojojinsa ya kuma yi mata ƙawanya.
Léta devátého Sedechiáše krále Judského, měsíce desátého, přitáhl Nabuchodonozor král Babylonský se vším vojskem svým k Jeruzalému, a oblehli jej.
2 A rana ta tara ga watan huɗu a shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya, sai aka huda katanga.
Jedenáctého pak léta Sedechiášova, měsíce čtvrtého, devátého dne měsíce, prolomeno jest město.
3 Sa’an nan dukan fadawan sarkin Babilon suka shiga suka zazzauna a Ƙofar Tsakiya. Wato, Nergal-Sharezer na Samgar-Nebo, Sarsekim wani babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da dukan sauran fadawan sarkin Babilon.
I vešla tam všecka knížata krále Babylonského, a posadila se v bráně prostřední: Nergalšaretser, Samgarnebu, Sarsechim, Rabsaris, Nergalšaretser, Rabmag, a všecka jiná knížata krále Babylonského.
4 Sa’ad da Zedekiya sarkin Yahuda da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu; suka bar birnin da dare ta hanyar lambun sarki, ta ƙofar da take tsakanin katanga biyu, suka nufi waje Araba.
Stalo se pak, když je uzřel Sedechiáš král Judský, a že všickni muži bojovní utekli, a vyšli v noci z města cestou zahrady královské skrze bránu mezi dvěma zdmi, ušel také cestou pouště.
5 Amma sojojin Babiloniyawa suka bi su, suka ci wa Zedekiya a filayen Yeriko. Suka kama shi suka kai shi wurin Nebukadnezzar a Ribla a ƙasar Hamat, inda aka yanke masa hukunci.
I honilo je vojsko Kaldejské, a postihli Sedechiáše na rovinách Jerišských, a jali jej a přivedli ho k Nabuchodonozorovi králi Babylonskému do Ribla, do země Emat. Kdežto učinil soud.
6 A can Ribla sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idanunsa aka kuma kashe dukan manyan mutanen Yahuda.
Nebo zmordoval král Babylonský syny Sedechiášovy v Ribla před očima jeho, i všecky nejpřednější Judské zmordoval král Babylonský.
7 Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya ya kuma buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babilon.
Oči pak Sedechiášovy oslepil, a svázav ho řetězy ocelivými, dovedl jej do Babylona.
8 Sai Babiloniyawa suka cinna wa fadar da kuma gidajen mutane wuta suka farfasa katangar Urushalima.
Dům také královský i domy toho lidu vypálili Kaldejští ohněm, a zdi Jeruzalémské pobořili.
9 Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya kwashi mutanen da suka rage a birnin zuwa zaman bauta a Babilon, tare da waɗanda suka riga suka tafi wurinsa, da kuma sauran mutanen.
Ostatek pak lidu, kterýž byl zůstal v městě, i poběhlce, kteříž byli ustoupili k němu, a jiný lid pozůstalý zavedl Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři, do Babylona.
10 Amma Nebuzaradan shugaban matsaran ya bar waɗansu matalauta a ƙasar Yahuda, su da ba su da kome; a lokacin kuwa ya ba su gonakin inabi da kuma filaye.
Toliko nejchaternějších z lidu, kteříž nikdež neměli nic, zanechal Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři, v zemi Judské, jimž rozdal vinice a rolí v ten den.
11 To, fa, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ba da wannan umarnai game da Irmiya ta wurin Nebuzaradan shugaban matsaran sarki cewa,
Přikázal pak Nabuchodonozor král Babylonský o Jeremiášovi Nebuzardanovi, hejtmanu nad žoldnéři, řka:
12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.”
Vezmi jej, a pilně ho opatruj, aniž jemu čiň co zlého, ale jakž tobě řekne, tak nalož s ním.
13 Saboda haka Nebuzaradan shugaban matsara, Nebushazban babban hafsa, Nergal-Sharezer bafade mai girma da sauran hafsoshin sarkin Babilon
Protož poslav Nebuzardan, hejtman nad žoldnéři, a Nebušazban, Rabsaris, a Nergalšaretser, Rabmag, a všickni hejtmané krále Babylonského,
14 suka aika aka kawo Irmiya daga filin matsar. Suka miƙa shi ga Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, don yă kai shi gidansa. Saboda haka ya zauna a can a cikin mutanensa.
Poslavše, pravím, vzali Jeremiáše z síně stráže, a dali jej Godoliášovi synu Achikamovu, syna Safanova, aby jej domů dovedl. Takž bydlil u prostřed lidu.
15 Yayinda aka kulle Irmiya a sansanin matsara, maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
Stalo se pak k Jeremiášovi slovo Hospodinovo, když ještě byl zavřín v síni stráže, řkoucí:
16 “Tafi ka faɗa wa Ebed-Melek mutumin Kush, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ina gab da cika maganata a kan wannan birni ta wurin masifa, ba wadata ba. A lokacin za tă cika a idanunka.
Jdi a rci Ebedmelechovi Mouřenínu, řka: Takto praví Hospodin zástupů, Bůh Izraelský: Aj, já způsobím to, aby došla slova má na město toto ke zlému a ne k dobrému, a splní se před oblíčejem tvým v ten den.
17 Amma zan kuɓutar da kai a wannan rana, in ji Ubangiji; ba zan ba da kai ga waɗanda kake tsoronsu ba.
Ale vysvobodím tě v ten den, dí Hospodin, aniž budeš vydán v ruku mužů těch, jejichž oblíčeje se lekáš.
18 Zan cece ka; ba za ka mutu ta wurin takobi ba amma za ka tsira da ranka, domin ka dogara gare ni, in ji Ubangiji.’”
Nebo jistotně vychvátím tě, abys od meče nepadl, a budeš míti život svůj místo kořisti, proto že jsi naději složil ve mně, dí Hospodin.

< Irmiya 39 >