< Irmiya 38 >

1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
Mattan oğlu Şefatya, Paşhur oğlu Gedalya, Şelemya oğlu Yehukal ve Malkiya oğlu Paşhur Yeremya'nın halka söylediği şu sözleri duydular:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
“RAB diyor ki, ‘Bu kentte kalan kılıçtan, kıtlıktan, salgından ölecek. Kildaniler'e gidense sağ kalacak, canını kurtarıp yaşayacak.’
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
RAB diyor ki, ‘Bu kent kesinlikle Babil Kralı'nın ordusuna teslim edilecek, Babil Kralı onu ele geçirecek.’”
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Önderler krala, “Bu adam öldürülmeli” dediler, “Çünkü söylediği bu sözlerle kentte kalan askerlerin ve halkın cesaretini kırıyor. Bu adam halkın yararını değil, zararını istiyor.”
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
Kral Sidkiya, “İşte o sizin elinizde” diye yanıtladı, “Kral size engel olamaz ki.”
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
Böylece Yeremya'yı alıp kralın oğlu Malkiya'nın muhafız avlusundaki sarnıcına halatlarla sarkıtarak indirdiler. Sarnıçta su yoktu, yalnız çamur vardı. Yeremya çamura battı.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
Sarayda görevli hadım Kûşlu Ebet-Melek Yeremya'nın sarnıca atıldığını duydu. Kral Benyamin Kapısı'nda otururken,
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
Ebet-Melek saraydan çıkıp kralın yanına gitti ve ona şöyle dedi:
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
“Efendim kral, bu adamların Peygamber Yeremya'ya yaptıkları kötüdür. Onu sarnıca attılar, orada açlıktan ölecek. Çünkü kentte ekmek kalmadı.”
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
Bunun üzerine kral, “Buradan yanına üç adam al, Peygamber Yeremya'yı ölmeden sarnıçtan çıkarın” diye ona buyruk verdi.
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Ebet-Melek yanına adamları alarak saray hazinesinin alt odasına gitti. Oradan eski bezler, yırtık pırtık giysiler alıp halatlarla sarnıca, Yeremya'ya sarkıttı.
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
Sonra Yeremya'ya, “Bu eski bezleri, yırtık giysileri halatlarla bağlayıp koltuklarının altına geçir” diye seslendi. Yeremya söyleneni yaptı.
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
Onu halatlarla çekip sarnıçtan çıkardılar. Yeremya muhafız avlusunda kaldı.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Kral Sidkiya Peygamber Yeremya'yı RAB'bin Tapınağı'nın üçüncü girişine getirterek, “Sana bir şey soracağım” dedi, “Benden bir şey gizleme.”
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
Yeremya, “Sana bir şey bildirirsem, beni öldürmeyecek misin?” diye karşılık verdi, “Üstelik öğüt versem bile beni dinlemeyeceksin.”
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
Kral Sidkiya, “Bize yaşam veren RAB'bin varlığı hakkı için seni öldürmeyeceğim, canının peşinde olan bu adamların eline seni teslim etmeyeceğim” diyerek gizlice ant içti.
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
Bunun üzerine Yeremya Sidkiya'ya şu karşılığı verdi: “İsrail'in Tanrısı, Her Şeye Egemen RAB Tanrı diyor ki, ‘Babil Kralı'nın komutanlarına teslim olursan, canın bağışlanacak, bu kent de ateşe verilmeyecek. Sen de ailen de sağ kalacaksınız.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
Ama Babil Kralı'nın komutanlarına teslim olmazsan, kent Kildaniler'e teslim edilecek, onu ateşe verecekler. Sen de onlardan kaçıp kurtulamayacaksın.’”
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
Kral Sidkiya, “Kildaniler'in tarafına geçen Yahudiler'den korkuyorum” dedi, “Kildaniler beni onların eline verebilir, onlar da bana kötü davranırlar.”
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
“Vermezler” diye yanıtladı Yeremya, “Lütfen sana aktardığım RAB'bin sözünü işit. O zaman sağ kalır, iyilik görürsün.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
Ama teslim olmak istemezsen, RAB bana şunu açıkladı:
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
Yahuda Kralı'nın sarayında kalan bütün kadınlar Babil Kralı'nın komutanlarına çıkarılacak. O kadınlar sana, “‘Güvendiğin insanlar Seni aldatıp yenilgiye uğrattı; Çamura battı ayakların, Güvendiğin insanlar seni bırakıp gitti’ diyecekler.
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
“Bütün karıların, çocukların Kildaniler'e teslim edilecek. Sen de onlardan kaçıp kurtulamayacak, Babil Kralı'nın eliyle yakalanacaksın. Bu kent ateşe verilecek.”
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
Sidkiya, “Ölmek istemiyorsan, konuştuklarımızı kimse duymasın” dedi,
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
“Görevliler seninle konuştuğumu duyup da gelir, ‘Krala ne söyledin, kral sana ne dedi, açıkla bize, bizden gizleme! Yoksa seni öldürürüz’ derlerse,
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
‘Beni Yonatan'ın evine geri gönderme, yoksa orada ölürüm diye krala yalvardım’ dersin.”
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
Bütün görevliler gelip Yeremya'yı sorguya çektiler. Yeremya kralın kendisine söylemesini buyurduğu her şeyi onlara anlattı. Sorguyu bıraktılar. Çünkü kralla yaptığı konuşma duyulmamıştı.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
Yeremya Yeruşalim'in ele geçirildiği güne dek muhafız avlusunda kaldı.

< Irmiya 38 >