< Irmiya 38 >

1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
UShefathiya indodana kaMathani, loGedaliya indodana kaPashuri, loJukali indodana kaShelemiya, loPashuri indodana kaMalikiya, sebezwile amazwi uJeremiya ayewakhuluma kubo bonke abantu esithi:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
Itsho njalo iNkosi: Osala kulumuzi uzakufa ngenkemba, ngendlala, langomatshayabhuqe wesifo; kodwa ophuma aye kumaKhaladiya uzaphila, ngoba uzakuba lempilo yakhe ibe yimpango, aphile.
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
Itsho njalo iNkosi: Lumuzi uzanikelwa isibili esandleni sebutho lenkosi yeBhabhiloni, elizawuthumba.
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Iziphathamandla zasezisithi enkosini: Ake abulawe lumuntu, ngoba ngalindlela uyekethisa izandla zamadoda empi asele kulumuzi, lezandla zabo bonke abantu, ngokukhuluma kibo amazwi anje; ngoba lumuntu kadingi ukuthula kwalababantu, kodwa okubi.
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
Inkosi uZedekhiya yasisithi: Khangela, usesandleni senu, ngoba inkosi kayilakho okuphambene lani ngalutho.
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
Basebemthatha uJeremiya, bamphosela emgodini kaMalikiya indodana yenkosi, owawusegumeni lentolongo, bamehlisa uJeremiya ngamagoda; kwakungelamanzi emgodini, kodwa udaka; uJeremiya wasetshona odakeni.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
Kwathi uEbedimeleki umEthiyophiya indoda umthenwa, owayesendlini yenkosi, esizwa ukuthi uJeremiya bamfake emgodini (lapho inkosi yayihlezi esangweni lakoBhenjamini),
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
uEbedimeleki waphuma endlini yenkosi, wakhuluma lenkosi esithi:
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
Nkosi yami, nkosi, abantu laba benzile okubi ngakho konke abakwenze kuJeremiya umprofethi, abamphosele emgodini, ngoba uzakufa endaweni yakhe ngenxa yendlala, ngoba kakusekho isinkwa emzini.
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
Inkosi yasimlaya uEbedimeleki umEthiyophiya, isithi: Thatha lapha amadoda angamatshumi amathathu ngaphansi kwesandla sakho, umenyule uJeremiya umprofethi emgodini engakafi.
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Ngakho uEbedimeleki wathatha amadoda ngaphansi kwesandla sakhe, wangena endlini yenkosi waze waba ngaphansi kwesiphala, wathatha khona izidwedwe ezidabukileyo lezidwedwe ezigugileyo, wazehlisela kuJeremiya emgodini ngamagoda.
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
UEbedimeleki umEthiyophiya wasesithi kuJeremiya: Ake ufake izidwedwe ezidabukileyo lezigugileyo ngaphansi kwamakhwapha akho ngaphansi kwamagoda. UJeremiya wasesenza njalo.
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
Basebemdonsa uJeremiya ngamagoda, bamenyula emgodini. UJeremiya wasehlala egumeni lentolongo.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Inkosi uZedekhiya yasithuma yathatha uJeremiya umprofethi yamusa kuye, ekungeneni kwesithathu okusendlini yeNkosi. Inkosi yasisithi kuJeremiya: Ngizakubuza udaba, ungangifihleli lutho.
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
UJeremiya wasesithi kuZedekhiya: Uba ngikutshela, kawuyikungibulala lokungibulala yini? Loba ngikweluleka, kawuyikungilalela.
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
Inkosi uZedekhiya yasifunga kuJeremiya ekusithekeni isithi: Kuphila kukaJehova owasenzela lumphefumulo: Isibili kangiyikukubulala, futhi isibili kangiyikukunikela esandleni salamadoda adinga umphefumulo wakho.
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
UJeremiya wasesithi kuZedekhiya: Itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu wamabandla, uNkulunkulu kaIsrayeli: Uba uphuma isibili uye kuziphathamandla zenkosi yeBhabhiloni, umphefumulo wakho uzaphila, lalumuzi kawuyikutshiswa ngomlilo; uzaphila wena lendlu yakho.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
Kodwa uba ungaphumi uye kuziphathamandla zenkosi yeBhabhiloni, lumuzi uzanikelwa esandleni samaKhaladiya, awutshise ngomlilo; lawe kawuyikuphunyuka esandleni sawo.
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
Inkosi uZedekhiya yasisithi kuJeremiya: Ngiyawesaba amaJuda ahlubukele kumaKhaladiya, hlezi anginikele esandleni sawo, angiklolodele.
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
UJeremiya wasesithi: Kawayikukunikela; ake ulalele ilizwi leNkosi njengalelo engilikhuluma kuwe, khona kukulungele, futhi umphefumulo wakho uzaphila.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
Kodwa uba usala ukuphuma, yileli ilizwi iNkosi engibonise lona lokuthi:
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
Khangela-ke, bonke abesifazana abasele endlini yenkosi yakoJuda bazakhitshelwa kuziphathamandla zenkosi yeBhabhiloni, bathi: Abangane bakho bakukhuthazile, bakwehlula; inyawo zakho zitshone odakeni; babuyele emuva.
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
Njalo azakhuphela abafazi bonke bakho lamadodana akho kumaKhaladiya; lawe kawuyikuphunyuka esandleni sawo, kodwa uzabanjwa ngesandla senkosi yeBhabhiloni, lalumuzi uzawutshisa ngomlilo.
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
UZedekhiya wasesithi kuJeremiya: Kakungabi khona umuntu owaziyo lamazwi, khona ungayikufa.
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
Kodwa nxa iziphathamandla zisizwa ukuthi ngikhulume lawe, zize kuwe zithi kuwe: Ake usitshele, ubusithini enkosini, ungakufihli kithi, khona kasiyikukubulala; njalo inkosi ikhulumeni kuwe;
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
uzakuthi-ke kuzo: Mina ngiwise ukuncenga kwami phambi kwenkosi ukuthi ingangibuyiseli endlini kaJonathani ukuze ngifele khona.
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
Zasezifika zonke iziphathamandla kuJeremiya, zambuza; yena waziphendula njengawo wonke lamazwi inkosi ewalayileyo. Zasezithula kuye, ngoba udaba lwalungezwakali.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
UJeremiya wasehlala egumeni lentolongo kwaze kwaba lusuku iJerusalema eyathunjwa ngalo; wayekhona lapho iJerusalema ithunjwa.

< Irmiya 38 >