< Irmiya 38 >

1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
Or Saphatias, fils de Mathan, et Gédélias, fils de Phassur, et Juchal, fils de Sélémias, et Phassur, fils de Melchias, entendirent les paroles que Jérémie adressait à tout le peuple, disant:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
Voici ce que dit le Seigneur: Quiconque demeurera dans cette cité mourra par le glaive, et par la famine et par la peste; mais celui qui s’enfuira vers les Chaldéens vivra, et son âme sera saine et sauve, et il vivra.
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
Voici ce que dit le Seigneur: En étant livrée, cette cité sera livrée en la main de l’armée du roi de Babylone, et il la prendra.
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Et les princes dirent au roi: Nous vous prions que cet homme soit mis à mort, car c’est à dessein qu’il affaiblit les mains des hommes de guerre qui sont demeurés dans cette cité, et les mains de tout le peuple, leur disant ces paroles; vu que cet homme ne cherche pas la paix de ce peuple, mais son malheur.
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
Et le roi Sédécias dit: Voici qu’il est entre vos mains; car il n’est pas juste que le roi vous refuse quelque chose.
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
Ils prirent donc Jérémie et le jetèrent dans la fosse de Melchias, fils d’Amélech, qui était dans le vestibule de la prison; et ils descendirent Jérémie avec des cordes dans cette fosse dans laquelle il n’y avait pas d’eau, mais de la boue; c’est pourquoi Jérémie descendit dans la boue.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
Mais Abdémélech, l’Ethiopien, eunuque qui était dans la maison du roi, apprit qu’on avait jeté Jérémie dans la fosse; or le roi était assis à la porte de Benjamin.
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
Et Abdémélech sortit de la maison du roi, et parla au roi, disant:
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
Mon Seigneur roi, ces hommes ont mal agi en tout ce qu’ils ont fait contre Jérémie, le prophète, le jetant dans la fosse afin qu’il y meure de faim, car il n’y a plus de pain dans la cité.
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
C’est pourquoi le roi ordonna à Abdémélech, l’Ethiopien, disant: Prends avec toi trente hommes, et ôte Jérémie, le prophète, de la fosse, avant qu’il meure.
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Abdémélech donc, ayant pris ces hommes avec lui, entra dans la maison du roi, dans un lieu qui était sous le cellier; et il en tira de vieilles étoffes et de vieux chiffons qui étaient pourris, et les descendit jusqu’à Jérémie avec des cordes.
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
Et Abdémélech, l’Ethiopien, dit à Jérémie: Mets ces vieilles étoffes et ces chiffons déchirés et pourris sous tes aisselles et sur les cordes. Jérémie fit donc ainsi.
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
Et ils enlevèrent Jérémie avec les cordes, et ils le tirèrent de la fosse; mais Jérémie demeura dans le vestibule de la prison.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Et le roi Sédécias envoya, et fit venir vers lui Jérémie, le prophète, à la troisième porte qui était dans la maison du Seigneur; et le roi dit à Jérémie: Moi je te demande une chose; ne me cache rien.
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
Or Jérémie dit à Sédécias: Si je vous annonce la vérité, est-ce que vous ne me tuerez pas? et si je vous donne un conseil, vous ne m’écouterez pas.
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
Le roi Sédécias jura donc à Jérémie secrètement, disant: Le Seigneur vit! qui nous a fait cette âme, si je te fais mourir, et si je te livre aux mains de ces hommes qui cherchent ton âme.
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
Et Jérémie dit à Sédécias: Voici ce que dit le Seigneur des armées, le Dieu d’Israël: Si tu sors pour aller voiries princes du roi de Babylone, ton âme vivra, et le feu ne sera pas mis à cette cité, et tu seras sauvé, ainsi que ta maison.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
Mais si tu ne sors pas vers les princes du roi de Babylone, cette cité sera livrée aux mains des Chaldéens, et ils y mettront le feu, et toi, tu n’échapperas pas de leurs mains.
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
Et le roi Sédécias dit à Jérémie: Je suis en peine à cause des Juifs qui ont passé du côté des Chaldéens; dans la crainte que je ne sois livré entre leurs mains, et qu’ils ne se jouent de moi.
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
Mais Jérémie répondit: On ne vous livrera pas; écoutez, je vous prie, la voix du Seigneur que je vous annonce; et bien vous sera, et votre âme vivra.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
Si vous ne voulez point sortir, voici ce que le Seigneur m’a montré:
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
Voilà que toutes les femmes qui seront demeurées dans la maison du roi de Juda seront conduites aux princes du roi de Babylone; et elles diront elles-mêmes: Ils vous ont séduit, et ils ont prévalu contre vous, les hommes qui vivaient en paix avec vous; ils vous ont plongé dans la fange et ont mis vos pieds dans des lieux glissants, et ils se sont retirés de vous.
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
Et toutes vos femmes et vos enfants seront conduits aux Chaldéens; et vous n’échapperez pas à leurs mains, mais vous serez pris dans la main du roi de Babylone; et cette cité, il y mettra le feu.
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
Sédécias dit donc à Jérémie: Que personne ne sache ces paroles que tu m’as dites, et tu ne mourras pas.
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
Mais si les princes apprennent que je t’ai parlé, et qu’ils viennent te dire: Fais-nous connaître ce que tu as dit au roi, ne nous cache rien, et nous ne te tuerons pas, et ce que t’a dit le roi;
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
Tu leur diras: Moi j’ai répandu mes prières devant le roi, afin qu’il ne me fît pas ramener dans la maison de Jonathan; car j’y mourrais.
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
Tous les princes vinrent donc vers Jérémie et l’interrogèrent, et il parla selon tout ce que le roi lui avait ordonné, et ils le laissèrent en paix; car rien n’avait été entendu.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
Or, Jérémie demeura dans le vestibule de la prison jusqu’au jour auquel fut prise Jérusalem; car il arriva que Jérusalem fut prise.

< Irmiya 38 >