< Irmiya 38 >

1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
Mais Séphatia fils de Mattan, et Guédalia fils de Pashur, et Jucal fils de Sélemja, et Pashur fils de Malkija, entendirent les paroles que Jérémie prononçait à tout le peuple, en disant:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
Ainsi a dit l'Eternel: celui qui demeurera dans cette ville mourra par l'épée, par la famine, ou par la mortalité, mais celui qui sortira vers les Caldéens vivra, et son âme lui sera pour butin, et il vivra.
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
Ainsi a dit l'Eternel: cette ville sera livrée certainement à l'armée du Roi de Babylone, et il la prendra.
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Et les principaux dirent au Roi: qu'on fasse mourir cet homme; car par ce moyen il rend lâches les mains des hommes de guerre qui sont demeurés de reste dans cette ville, et les mains de tout le peuple, en leur disant de telles paroles; parce que cet homme ne cherche point la prospérité de ce peuple, mais le mal.
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
Et le Roi Sédécias dit: voici, il est entre vos mains; car le Roi ne peut rien par dessus vous.
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
Ils prirent donc Jérémie, et le jetèrent dans la fosse de Malkija, fils de Hammélec, laquelle était dans la cour de la prison, et ils descendirent Jérémie avec des cordes dans cette fosse où il n'y avait point d'eau, mais de la boue; et ainsi Jérémie enfonça dans la boue.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
Mais Hebed-mélec Cusien, Eunuque, qui était dans la maison du Roi, apprit qu'ils avaient mis Jérémie dans cette fosse; et le Roi était assis à la porte de Benjamin.
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
Et Hebed-mélec sortit de la maison du Roi, et parla au Roi, en disant:
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
Ô Roi mon Seigneur! ces hommes-là ont mal fait dans tout ce qu'ils ont fait contre Jérémie le Prophète, en le jetant dans la fosse, car il serait déjà mort de faim dans le lieu où il était, parce qu'il n'[y a] plus de pain dans la ville.
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
C'est pourquoi le Roi commanda à Hebed-mélec Cusien, en disant: prends d'ici trente hommes sous ta conduite, et fais remonter hors de la fosse Jérémie le Prophète, avant qu'il meure.
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Hebed-mélec donc prit ces hommes sous sa conduite, et entra dans la maison du Roi au lieu qui est sous la Trésorerie, d'où il prit de vieux lambeaux et de vieux haillons, et les descendit avec des cordes à Jérémie dans la fosse;
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
Et Hebed-mélec Cusien dit à Jérémie: mets ces vieux lambeaux et ces haillons sous les aisselles de tes bras, au dessous des cordes; et Jérémie fit ainsi.
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
Ainsi ils tirèrent Jérémie dehors avec les cordes, et le firent remonter hors de la fosse; et Jérémie demeura dans la cour de la prison.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Et le Roi Sédécias envoya, et fit amener vers lui Jérémie le Prophète à la troisième entrée qui était dans la maison de l'Eternel. Et le Roi dit à Jérémie: je vais te demander une chose, ne m'en cèle rien.
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
Et Jérémie répondit à Sédécias: quand je te l'aurai déclarée, n'est-il pas vrai que tu me feras mourir? et quand je t'aurai donné conseil, tu ne m'écouteras point.
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
Alors le Roi Sédécias jura secrètement à Jérémie, en disant: l'Eternel [est] vivant, qui nous a fait cette âme-ci, que je ne te ferai point mourir, et que je ne te livrerai point entre les mains de ces gens-là qui cherchent ta vie.
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
Alors Jérémie dit à Sédécias: ainsi a dit l'Eternel, le Dieu des armées, le Dieu d'Israël: si tu sors volontairement pour aller vers les principaux du Roi de Babylone, ta vie te sera conservée, et cette ville ne sera point brûlée au feu, et tu vivras toi et ta maison.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
Mais si tu ne sors pas vers les principaux du Roi de Babylone, cette ville sera livrée entre les mains des Caldéens, qui la brûleront au feu; et tu n'échapperas point de leurs mains.
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
Et le Roi Sédécias dit à Jérémie: j'appréhende à cause des Juifs qui se sont rendus aux Caldéens, qu'on ne me livre entre leurs mains, et qu'ils ne se moquent de moi.
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
Et Jérémie lui répondit: on ne te livrera point à eux; je te prie, écoute la voix de l'Eternel dans ce que je te dis, afin que tu t'en trouves bien, et que tu vives.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
Que si tu refuses de sortir, voici ce que l'Eternel m'a fait voir,
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
C'est que, voici, toutes les femmes qui sont demeurées de reste dans la maison du Roi de Juda, seront menées dehors aux principaux du Roi de Babylone, et elles diront que ceux qui ne te prédisaient que paix, t'ont incité, et t'ont gagné; tellement que tes pieds sont enfoncés dans la boue, s'étant reculés en arrière.
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
Ils s'en vont donc mener dehors aux Caldéens toutes tes femmes et tes enfants, et tu n'échapperas point de leurs mains, mais tu seras pris, pour être livré entre les mains du Roi de Babylone, et tu seras cause que cette ville sera brûlée au feu.
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
Alors Sédécias dit à Jérémie: que personne ne sache rien de ces paroles, et tu ne mourras point.
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
Et si les principaux entendent que je t'ai parlé, et qu'ils viennent vers toi, et te disent: déclare-nous maintenant ce que tu as dit au Roi, et ce que le Roi a dit, ne nous en cèle rien, et nous ne te ferons point mourir;
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
Tu leur diras: j'ai présenté ma supplication devant le Roi, afin qu'il ne me fît point ramener dans la maison de Jéhonathan pour y mourir.
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
Tous les principaux donc vinrent vers Jérémie, et l'interrogèrent; mais il leur fit un rapport conforme à toutes les paroles que le Roi [lui] avait commandé de dire; et ils cessèrent de lui parler, car on n'avait rien su de cette affaire.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
Ainsi Jérémie demeura dans la cour de la prison, jusqu’au jour que Jérusalem fut prise, et il y était lorsque Jérusalem fut prise.

< Irmiya 38 >