< Irmiya 38 >
1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
Shephatiah son of Mattan, Gedaliah son of Pashhur, Jucal son of Shelemiah, and Pashhur son of Malchijah heard what Jeremiah was telling everyone:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
This is what the Lord says: Anyone who remains in this city will die from war and famine and disease, but anyone who goes over to the Babylonians will live. Their reward will be to save their lives.
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
This is what the Lord says: Be sure of this—Jerusalem will be handed over to the army of the king of Babylon. He is going to capture it.
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
The officers told the king, “This man deserves to die because he's demoralizing the defenders left in the city, and all the people too, by telling them this. This man isn't trying to help these people, he's only going to destroy them.”
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
“Well, you can do whatever you want to him,” King Zedekiah replied. “I can't stop you.”
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
So they took Jeremiah and put him in the cistern belonging to Malchiah, the king's son, which was in the guard's courtyard. They lowered Jeremiah down with ropes into the cistern. It didn't have any water, only mud, and Jeremiah sank into the mud.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
Ebed-melech the Cushite, a royal official in the king's palace, found out that they had put Jeremiah in the cistern. The king was sitting at the Benjamin Gate,
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
so Ebed-melech left the palace and went to talk to the king
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
“My lord the king, all these terrible things these men have done to Jeremiah the prophet are evil. They've put him in the cistern, and he'll starve to death there because there's no more bread left in the city.”
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
So the king gave the order to Ebed-melech the Cushite, “Take thirty men with you and go and pull Jeremiah the prophet out of the cistern before he dies.”
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Ebed-melech took the men and went to the storehouse under the palace. He took some rags and old clothes from there and then went to the cistern where he lowered them with ropes to Jeremiah.
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
Ebed-melech the Cushite called down to Jeremiah, “Put these rags and old clothes under your arms to protect you from the ropes.” Jeremiah did so,
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
and using the ropes they pulled him up and took him out of the cistern. Jeremiah stayed there in the guard's courtyard.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Then King Zedekiah sent for Jeremiah the prophet and met him at the third Temple entrance. “I need to ask you something,” the king told Jeremiah. “You mustn't hide anything from me.”
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
“If I tell you then you'll definitely have me killed,” Jeremiah replied. “Even if I were to give you advice, you wouldn't listen to me anyway.”
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
King Zedekiah solemnly promised Jeremiah in private, “As the Lord lives, who gave us this life, I won't have you killed, and I won't hand you over to those who want to kill you.”
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
Then Jeremiah told Zedekiah, “This is what the Lord God Almighty, the God of Israel, says: ‘If you hand yourself over to the officers of the king of Babylon, then you'll live. Jerusalem won't be burned down, and you and your family will survive.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
But if you don't hand yourself over to the officers of the king of Babylon, then this city will be given to the Babylonians. They will burn it down, and you yourself won't escape being captured.”
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
But King Zedekiah said to Jeremiah, “I am afraid of the those people of Judah who have gone over to the Babylonians, because the Babylonians might hand me over the them so they could abuse me.”
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
“They won't hand you over,” Jeremiah replied. “If you obey what the Lord says by doing what I tell you, then things will go well for you and you'll live.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
But if you refuse to hand yourself over, this is what the Lord has told me:
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
All the women who are left in the palace of the king of Judah will be led out and handed over to the officials of the king of Babylon Those women will say: ‘Those good friends of yours! You were taken in by them and conquered by them. Your feet got stuck in the mid, so they abandoned you.’
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
All your wives and children will be handed over to the Chaldeans. And you yourself will not escape, for you will be captured by the king of Babylon, and Jerusalem will be burned down.”
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
Zedekiah warned Jeremiah, “Nobody can find out about this conversation, otherwise you'll die.
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
If the officers find out that I've talked with you, and they come and ask you, ‘Tell us what you and the king were talking about! Don't hide anything from us, or we'll kill you;’
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
then you are to tell them, ‘I was asking the king to grant my request not to return me to the house of Jonathan to die there.’”
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
When all the officers came to Jeremiah wanting to know, he repeated to them exactly what the king had told him to say. So they didn't ask him anything more because no one had heard what had been said.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
Jeremiah remained there in the guard's courtyard until the day Jerusalem was captured.