< Irmiya 38 >

1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
Shefatia wuod Matan, Gedalia wuod Pashur, Jehukal wuod Shelemia, kod Pashur wuod Malkija nowinjo gima Jeremia ne nyiso ji duto sa mane owacho ni,
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
“Ma e gima Jehova Nyasaye wacho: ‘Ngʼato angʼata modak e dala maduongʼni noneg gi ligangla, kech kata masira, to ngʼato angʼata manodhi ir jo-Babulon nobed mangima. Notony gi ngimane; mi nobed mangima.’
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
Kendo ma e gima Jehova Nyasaye wacho: ‘Dala maduongʼni nyaka chiwne jolweny mar ruodh Babulon ma nokawe.’”
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Eka jotelo nowachone ruoth niya, “Ngʼatni onego negi. Onyoso chuny jolweny modongʼ e dala maduongʼ ni, kaachiel gi ji duto, gi gigo mowachonegi. Ngʼatni ok dwar dhi maber mar jogi to mana kethruokgi.”
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
Ruoth Zedekia nowacho niya, “En e lwetu. Onge gima ruoth nyalo timo mondo okwed wachu.”
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
Omiyo negikawo Jeremia ma giketo e bur mar Malkija, wuod ruoth, mane nitiere e laru mar jarito. Ne giloro Jeremia gi tonde ei burno; ne onge pi e iye, chwodho ema ne nitie, kendo Jeremia nonimo ei chwodho.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
To Ebed-Melek, ja-Kush, ma jatelo e kar dak ruoth, nowinjo nine giseketo Jeremia ei bur. Ka ruoth ne obet e Dhoranga Benjamin,
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
Ebed-Melek nowuok oa e kar dak ruoth kendo owachone ni,
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
“Jaduongʼ ma ruodha, jogi osetimo gima mono kuom gigo duto magisetimone janabi Jeremia. Giwite e bur, kama kech biro nege motho ka makati duto orumo e dala maduongʼ.”
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
Eka ruoth nomiyo Ebed-Melek ja-Kush chik, “Kaw chwo piero adek koa kae kendo ugol janabi Jeremia e bur kapok otho.”
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Omiyo Ebed-Melek nokawo jogo kendo odhigo e agola manie bwo kar keno mar dala ruoth. Ne okawo lewni moyiech kod lewni moti kanyo kendo nolorogi piny gi tol ne Jeremia ei bur.
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
Ebed-Melek ja-Kush nowacho ne Jeremia niya, “Ket lewni mokengoregi kod lewni moti e yuothi mondo kik tol ridhi.” Jeremia notimo kamano,
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
mine giywaye gi tol ma gigole oko mar bur. Kendo Jeremia nodongʼ e laru mar jarito.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Eka Ruoth Zedekia nooro wach mondo okelne janabi Jeremia kendo nokelnego e kar donjo mar adek mar hekalu mar Jehova Nyasaye. Ruoth nowachone niya, “Adhi penji gimoro. Kik ipanda wach.”
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
Jeremia nowachone Zedekia niya, “Ka adwoki, donge ibiro nega? Kata ka anangʼadni rieko, bende iniwinja.”
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
To Ruoth Zedekia nokwongʼore gi kwongʼruokni lingʼ-lingʼ ne Jeremia: “Akwongʼora gi nying Jehova Nyasaye mangima, mosemiyowa muya, ok ananegi kata chiwi ne jogo madwaro ngimani.”
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
Eka Jeremia nowachone Zedekia niya, “Ma e gima Jehova Nyasaye Maratego, ma Nyasach Israel, wacho: ‘Ka ichiwori ne jotelo mag ruodh Babulon, ngimani noweni kendo dala maduongʼni ok nowangʼ, in kod joodi unubed mangima.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
To ka ok ichiwori ne jotend ruodh Babulon, dala maduongʼni nomi jo-Babulon kendo giniwangʼe; un uwegi ok unutony e lwetgi.’”
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
Ruoth Zedekia nowachone Jeremia niya, “Aluoro jo-Yahudi mosedhi ir jo-Babulon, nimar jo-Babulon nyalo chiwa e lwetgi mi gisanda.”
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
Jeremia nodwoke niya, “Ok ginichiwi.” Luor Jehova Nyasaye kitimo gima anyisi. Eka inine maber, kendo ngimani noweni.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
To ka itamori chiwori, ma e gima Jehova Nyasaye osefwenyona:
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
Mon duto mane odongʼ kar dak mar ruodh Juda nokelne jotelo mar ruodh Babulon. Mon-go nowachni ni: Osiepegi mane igenogo nowuondi kendo noloyi. Tiendegi oselingʼore e chwodho; osiepegi oseweyi.
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
“Mondeu duto kod nyithindu nokelne jo-Babulon. Un uwegi ok unutony e lwetgi to enomaku gi ruodh Babulon; kendo dala maduongʼni nowangʼ mapodhi.”
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
Eka Zedekia nowachone Jeremia niya, “Kik iwe ngʼato ongʼe twak-wani, ka ok kamano to inyalo tho.
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
Ka jotelo owinjo nine awuoyo kodi, kendo gibiro iri ma giwacho, ‘Nyiswa gima ne iwachone ruoth kendo gima ruoth nowachoni; kik ipandwa ka ok kamano to wabiro negi,’
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
to nyisgi ni, ‘Ne asayo ruoth mondo kik oora adog e od Jonathan mondo atho kanyo.’”
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
Jotelo duto nobiro ir Jeremia mi gipenje, kendo nonyisogi gik moko duto mane ruoth ochike mondo awachi. Omiyo onge gima negichako ginyise, nimar onge ngʼama nowinjo twakgi gi ruoth.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
Kendo Jeremia nodongʼ e laru mar jarito nyaka odiechiengʼ ma Jerusalem nokaw. Ma e kaka Jerusalem ne okaw:

< Irmiya 38 >