< Irmiya 38 >

1 Shefatiya ɗan Mattan, Gedaliya ɗan Fashhur, Yukal ɗan Shelemiya da Fashhur ɗan Malkiya ya ji abin da Irmiya yana faɗa wa dukan mutane sa’ad da ya ce,
Og Sefatja, Matthans Søn, og Gedalja, Paskurs Søn, og Jukal, Selemjas Søn, og Paskur, Malkias Søn, hørte de Ord, som Jeremias talte til alt Folket, der han sagde:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba, amma duk wanda ya je wurin Babiloniyawa zai rayu. Zai tsira da ransa, ya rayu.’
Saa siger Herren: Hvo, som bliver i denne Stad, skal dø ved Sværdet, ved Hungeren og ved Pesten; men den, som gaar ud til Kaldæerne, han skal leve, og han skal have sit Liv som Bytte, saa at han skal blive i Live.
3 Kuma ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Tabbatacce za a ba da wannan birni ga sojojin sarkin Babilon, wanda zai ci shi.’”
Saa siger Herren: Denne Stad skal visselig gives i Kongen af Babels Hærs Haand, og han skal indtage den.
4 Sai fadawa suka ce wa sarki, “Ya kamata a kashe wannan mutum. Yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran mutane, ta wurin abubuwan da yake faɗa musu. Wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan sai dai wahala.”
Da sagde Fyrsterne til Kongen: Lad dog denne Mand dræbe, thi paa den Maade bringer han Hænderne paa Krigsmændene, som ere overblevne i denne Stad, og Hænderne paa hele Folket til at synke, idet han taler saadanne Ord til dem; thi denne Mand søger ikke dette Folks Bedste, men dets Ulykke.
5 “Yana a hannuwanku” Sarki Zedekiya ya amsa. “Sarki ba zai iya yin kome ya hana ku ba.”
Og Kong Zedekias sagde: Se, han er i eders Haand; thi Kongen formaar intet imod eder.
6 Saboda haka suka kama Irmiya suka sa a rijiyar da ba ruwa a ciki ta Malkiya, ɗan sarki, wadda take a sansanin matsara. Suka saukar da Irmiya cikin rijiyar da ba ruwa da igiya; babu ruwa a cikinta, sai laka, Irmiya ya nutse cikin laka.
Da toge de Jeremias og kastede ham i Malkias, Meleks Søns, Hule, som var i Fængselets Forgaard, og nedlode Jeremias ved Reb, og i Hulen var der ikke Vand, men Dynd, og Jeremias sank ned i Dyndet.
7 Amma Ebed-Melek mutumin Kush, wani hafsa a fada, ya ji cewa sun sa Irmiya a rijiyar da ba ruwa. Yayinda sarki yana zama a Ƙofar Benyamin,
Der Kusiten Ebed-Melek, en Mand, som var Hofmand og var i Kongens Hus, hørte, at man havde kastet Jeremias i Hulen, og Kongen sad i Benjamins Port,
8 Ebed-Melek ya fita daga fadar ya ce masa,
da gik Ebed-Melek ud af Kongens Hus, og han talte med Kongen og sagde:
9 “Ranka yă daɗe sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu a duk abin da suka yi wa Irmiya annabi. Sun jefa shi cikin rijiyar da ba ruwa, inda zai mutu da yunwa gama ba sauran wani burodi a birnin.”
Min Herre Konge: Disse Mænd have gjort ilde i alt det, de have gjort imod Profeten Jeremias, som de kastede i Hulen, saa at han der, hvor han er, maa dø af Hunger; thi her er ikke Brød i Staden mere.
10 Sai sarki ya umarce Ebed-Melek mutumin Kush, “Ka ɗauko mutane talatin daga nan ku fid da Irmiya annabi daga rijiyar kafin ya mutu.”
Da befalede Kongen Kusiten Ebed-Melek og sagde: Tag tredive Mand herfra med dig, og drag Profeten Jeremias op af Hulen, førend han dør.
11 Saboda haka Ebed-Melek ya ɗauki mutane tare da shi suka shiga ɗaki a ƙarƙashin baitulmali a cikin fada. Ya ɗauko waɗansu tsofaffin tsummoki da tsofaffi riguna daga can ya kuma zurara su da igiya wa Irmiya a cikin rijiyar.
Og Ebed-Melek tog Mændene med sig og gik ind i Kongens Hus, hen under Forraadskammeret, og tog derfra nogle gamle Pjalter og gamle Klude og lod dem gaa ned til Jeremias i Hulen med Rebene.
12 Ebed-Melek mutumin Kush ya ce wa Irmiya, “Ka sa waɗannan tsummoki da tsofaffin rigunan a hammatarka, ya zarga igiya.” Irmiya ya yi haka,
Og Kusiten Ebed-Melek sagde til Jeremias: Læg dog de gamle Pjalter og Klude om dine Aksler under Rebene; og Jeremias gjorde saaledes.
13 suka kuma ja shi sama da igiya suka fid da shi daga rijiyar. Irmiya kuwa ya zauna a sansanin matsara.
Og de droge Jeremias op med Rebene og førte ham op af Hulen; og Jeremias blev i Fængselets Forgaard.
14 Sai Sarki Zedekiya ya aika a kawo Irmiya annabi, ya sa aka kawo shi a ƙofa ta uku ta haikalin Ubangiji. Sai sarki ya ce wa Irmiya, “Zan tambaye ka wani abu, kada ka ɓoye mini wani abu.”
Og Kong Zedekias sendte Bud og lod Profeten Jeremias hente til sig, hen til den tredje Indgang til Herrens Hus; og Kongen sagde til Jeremias: Jeg vil spørge dig om noget, du maa intet dølge for mig.
15 Irmiya ya ce wa Zedekiya, “In na ba ka amsa, ba za ka kashe ni ba? Ko da na ba ka shawara, ba za ka saurare ni ba.”
Og Jeremias sagde til Zedekias: Naar jeg forkynder dig det, mon du da ikke vil lade mig dræbe? og naar jeg giver dig Raad, saa vil du dog ikke høre mig!
16 Amma Sarki Zedekiya ya yi wannan rantsuwa a kaɗaice ga Irmiya cewa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya ba mu numfashi, ba zan kashe ka ko in ba da kai ga waɗanda suke neman ranka ba.”
Da svor Kong Zedekias Jeremias i Løndom og sagde: Saa sandt Herren lever, som har skabt os denne Sjæl, saa vil jeg ikke dræbe dig, ej heller give dig i disse Mænds Haand, som søge efter dit Liv.
17 Sa’an nan Irmiya ya ce wa Zedekiya, “Ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon, za a bar ka da rai ba za a kuma ƙone wannan birni ba; da kai da iyalinka za ku rayu.
Og Jeremias sagde til Zedekias: Saa siger den Herre Zebaoths Gud, Israels Gud: Dersom du godvilligt gaar ud til Kongen af Babels Fyrster, da skal du beholde Livet, og denne Stad skal ikke opbrændes med Ild; og du skal leve, du og dit Hus.
18 Amma in ba ka miƙa wuya ga hafsoshin sarkin Babilon ba, za a ba da wannan birni ga Babiloniyawa za su kuma cinna mata wuta; kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba.’”
Men dersom du ikke gaar ud til Kongen af Babels Fyrster, da skal denne Stad gives i Kaldæernes Haand, og de skulle opbrænde den med Ild; og du skal ikke undkomme af deres Haand.
19 Sarki Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawan da suka tafi wurin Babiloniyawa, gama Babiloniyawa mai yiwuwa su ba da ni gare su su kuma wulaƙanta ni.”
Og Kong Zedekias sagde til Jeremias: Jeg frygter for de Jøder, som ere gaaede over til Kaldæerne, at man maaske vil give mig i deres Haand, og at disse ville handle ilde med mig.
20 Irmiya ya ce, “Ba za su ba da kai ba, ka yi biyayya ga Ubangiji ta wurin yin abin da na faɗa maka. Ta haka zai zama maka da amfani, za ka kuwa rayu.
Og Jeremias sagde: Man vil ikke give dig til Pris; hør dog paa Herrens Røst i det, som jeg taler til dig, og det skal gaa dig vel, og du skal beholde Livet.
21 Amma in ka ƙi miƙa wuya, ga abin da Ubangiji ya bayyana mini.
Men dersom du vægrer dig ved at gaa ud, saa er her det Ord, som Herren har ladet mig se:
22 Za a fitar da dukan matan da suka ragu a fadan sarkin Yahuda wa hafsoshin sarkin Babilon. Waɗannan mata za su ce maka, “‘Sun ruɗe ka suka kuma rinjaye ka, waɗannan abokanka. Ƙafafunka sun nutse a cikin laka; abokanka sun yashe ka.’
Se, alle Kvinderne, som ere blevne tilbage i Judas Konges Hus, føres ud til Kongen af Babels Fyrster og sige: Dine gode Venner have forført dig og have faaet Overhaand over dig, dine Fødder ere nedsunkne i Skarnet, medens hine ere vegne tilbage.
23 “Za a kawo dukan matanka da’ya’yanka wa Babiloniyawa. Kai kanka ba za ka tsira daga hannuwansu ba amma za su sa sarkin Babilon zai kama ka; za a kuma ƙone wannan birni.”
Og man skal føre alle dine Hustruer og dine Børn ud til Kaldæerne, og du selv skal ikke undkomme fra deres Haand, men gribes ved Kongen af Babels Haand, og denne Stad skal du bringe til at blive opbrændt med Ild.
24 Sai Zedekiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan zance, in ba haka ba za ka mutu.
Og Zedekias sagde til Jeremias: Lad ingen vide disse Ord, saa skal du ikke dø.
25 In fadawa suka ji cewa na yi magana da kai, suka kuma zo wurinka suka ce, ‘Faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da kuma abin da sarki ya faɗa maka; kada ka ɓoye mana, in ba haka za mu kashe ka,’
Og naar Fyrsterne høre, at jeg har talt med dig, og de komme til dig og sige til dig: Kære, kundgør os, hvad du har talt til Kongen, dølg det ikke for os, og vi ville ikke dræbe dig; og hvad Kongen har talt til dig:
26 sai ka ce musu cewa, ‘Na roƙi sarki kada yă mai da ni gidan Yonatan in mutu a can.’”
Saa skal du sige til dem: Jeg lod min ydmyge Begæring komme ind for Kongens Ansigt, at man ikke maatte føre mig igen i Jonathans Hus, at dø der.
27 Dukan fadawa kuwa suka zo wurin Irmiya suka tambaye shi, ya kuma faɗa musu dukan abin da sarki ya umarce shi ya faɗa. Saboda haka ba su ƙara ce masa kome ba, gama ba wanda ya ji zance da suka yi da sarki.
Da kom alle Fyrsterne til Jeremias og spurgte ham, og han svarede dem efter alle disse Ord, som Kongen havde befalet; da tav de og lode ham i Ro; thi Ordet fik de ej at høre.
28 Irmiya kuwa ya zauna a sansanin masu gadi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi. Ga yadda aka ci Urushalima,
Og Jeremias blev i Fængselets Forgaard indtil den Dag, da Jerusalem blev indtaget. Og det skete, da Jerusalem blev indtaget, —

< Irmiya 38 >