< Irmiya 37 >

1 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
Og Sedekias, Josias' sønn, blev konge efter Konja, Jojakims sønn for Babels konge Nebukadnesar hadde satt ham til konge i Juda land.
2 Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
Men han og hans tjenere og landets folk hørte ikke på Herrens ord, som han talte ved profeten Jeremias.
3 Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
Og kong Sedekias sendte Jehukal, Selemjas sønn, og presten Sefanja, Ma'asejas sønn, til profeten Jeremias og lot si: Bed for oss til Herren vår Gud!
4 To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
Jeremias gikk dengang inn og ut blandt folket; de hadde ennu ikke satt ham i fengsel.
5 Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
Og Faraos hær hadde da draget ut fra Egypten, og da kaldeerne, som holdt Jerusalem kringsatt, spurte det, drog de bort fra Jerusalem.
6 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
Da kom Herrens ord til profeten Jeremias, og det lød så:
7 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
Så sier Herren, Israels Gud: Så skal I si til Judas konge, som sendte eder til mig for å spørre mig: Se, Faraos hær, som har draget ut for å komme eder til hjelp, skal vende tilbake til sitt land, Egypten,
8 Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
og kaldeerne skal komme igjen og stride mot denne by, og de skal innta den og brenne den op med ild.
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
Så sier Herren: I må ikke dåre eder selv og si: Kaldeerne skal visselig dra bort fra oss! For de skal ikke dra bort;
10 Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
om I så slo hele kaldeernes hær som strider mot eder, og det bare blev nogen hårdt sårede tilbake iblandt dem, så skulde disse stå op, hver i sitt telt, og brenne denne by op med ild.
11 Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
Og da kaldeernes hær hadde draget bort fra Jerusalem for Faraos hærs skyld,
12 sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
da gikk Jeremias ut av Jerusalem midt iblandt folket for å gå til Benjamins land og hente sin arvelodd derfra.
13 Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
Og da han var i Benjamin-porten, så stod der en høvedsmann for vakten ved navn Jerija, sønn av Selemja, sønn av Hananja; han grep fatt i profeten Jeremias og sa: Du vil gå over til kaldeerne.
14 Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
Da sa Jeremias: Det er løgn; jeg vil ikke gå over til kaldeerne. Men Jerija hørte ikke på Jeremias, han grep ham og førte ham til høvdingene.
15 Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
Da blev høvdingene vrede på Jeremias og slo ham, og de satte ham i fangehuset, i statsskriveren Jonatans hus; for det hadde de gjort til fengsel.
16 Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
Da Jeremias var kommet i fangehullet, i kjelleren, og hadde sittet der i mange dager,
17 Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
sendte kong Sedekias bud og lot ham hente, og kongen spurte ham i sitt hus i lønndom og sa: Er det noget ord fra Herren? Jeremias svarte: Ja, det er. Og så sa han: Du skal bli gitt i Babels konges hånd.
18 Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
Derefter sa Jeremias til kong Sedekias: Hvad har jeg syndet mot dig og dine tjenere og dette folk, siden I har satt mig i fengsel?
19 Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
Og hvor er nu eders profeter, de som profeterte for eder og sa: Babels konge skal ikke komme over eder og over dette land?
20 Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
Og hør nu, herre konge! La min ydmyke bønn bæres frem for ditt åsyn og send mig ikke tilbake til statsskriveren Jonatans hus, forat jeg ikke skal dø der!
21 Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.
På kong Sedekias' bud holdt de Jeremias i varetekt i vaktgården og gav ham et brød til hver dag fra bakernes gate, inntil alt brødet i byen var fortært. Og Jeremias blev sittende i vaktgården.

< Irmiya 37 >