< Irmiya 37 >
1 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
Sédécias, fils de Josias, exerça la royauté à la place de Coniahou, fils de Joïakim; car Nabuchodonosor, roi de Babylone, l’avait établi roi dans le pays de Juda.
2 Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
Mais ni lui, ni ses serviteurs, ni le peuple du pays n’écoutèrent les paroles de l’Eternel, énoncées par l’organe du prophète Jérémie.
3 Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
Le roi Sédécias envoya dire au prophète Jérémie par léhoukhal, fils de Chélémia, et par Cefania, fils de Masséya, le prêtre: "De grâce, implore en notre faveur l’Eternel, notre Dieu."
4 To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
Or, Jérémie allait et venait au milieu du peuple, et on ne le tenait pas enfermé dans la prison.
5 Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
Cependant l’armée de Pharaon étant sortie de l’Egypte, les Chaldéens qui cernaient Jérusalem en furent informés et ils levèrent le siège de Jérusalem.
6 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
C’Est alors que la parole de l’Eternel fut adressée à Jérémie, le prophète, en ces termes:
7 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
"Ainsi parle l’Eternel, Dieu d’Israël: Voici ce que vous direz au roi de Juda qui vous envoie à moi pour me solliciter: Cette armée de Pharaon qui s’est mise en marche pour vous secourir, elle rebrousse chemin vers son pays, l’Egypte.
8 Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
Aussi les Chaldéens reviendront-ils pour attaquer cette ville, ils l’emporteront de vive force et la livreront aux flammes."
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
Ainsi parle l’Eternel: "Ne vous leurrez pas vous-mêmes en disant: Assurément, les Chaldéens partiront de chez nous, car ils ne partiront pas.
10 Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
Et dussiez-vous même tailler en pièces toute l’armée des Chaldéens qui combat contre vous, de sorte qu’il n’en restât que quelques hommes blessés par la lance, ceux-ci se redresseraient dans leur tente et mettraient le feu à cette ville!"
11 Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
Alors que l’armée des Chaldéens s’éloignait de Jérusalem à cause de l’armée de Pharaon,
12 sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
Jérémie se disposa à sortir de Jérusalem pour se rendre sur le territoire de Benjamin, et de là se glisser dans la foule.
13 Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
Mais s’étant présenté à la porte de Benjamin, il y rencontra un chef de poste du nom de Yriya, fils de Chélémia, fils de Hanania. Celui-ci arrêta le prophète Jérémie en disant: "Tu veux passer aux Chaldéens!"
14 Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
Jérémie répliqua: "C’Est faux! je ne passe pas aux Chaldéens!" Mais Yriya ne l’écouta point, il se saisit de Jérémie et l’amena aux officiers.
15 Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
Les officiers s’emportèrent contre Jérémie, le frappèrent et le firent incarcérer dans la maison de Jonathan, le secrétaire, transformée en prison.
16 Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
C’Est ainsi que Jérémie fut confiné dans la chambre souterraine, qui servait de dépôt, et il y demeura de longs jours.
17 Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
Or, le roi Sédécias l’envoya chercher et l’interrogea secrètement en son palais en lui disant: "Y a-t-il une communication de la part de l’Eternel?" Jérémie répondit: "Il y en a;" il ajouta: "Tu seras livré aux mains du roi de Babylone."
18 Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
Jérémie dit encore au roi Sédécias: "Quel crime ai-je commis contre toi, tes serviteurs et ce peuple, que vous m’ayez enfermé dans la maison de détention?
19 Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
Où sont donc vos prophètes qui vous ont fait cette prédiction: Jamais le roi de Babylone ne marchera contre vous et contre ce pays?
20 Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
Et maintenant écoute, de grâce, ô Seigneur roi, et laisse ma supplication arriver jusqu’à toi: Ne me fais pas rentrer dans la maison de Jonathan, le secrétaire, sans cela, ma mort est certaine."
21 Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.
Le roi Sédécias donna des ordres, à la suite desquels on mit Jérémie sous garde dans la cour de la geôle; et chaque jour on lui fournissait une miche de pain de la rue des boulangers, jusqu’au moment où le pain vint à manquer tout à fait dans la ville. Jérémie demeura donc dans la cour de la geôle.