< Irmiya 37 >
1 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
Le roi Sédécias, fils de Josias, régna à la place de Jéchonias, fils de Joakim, — Nabuchodonosor, roi de Babylone, l’avait établi roi sur le pays de Juda. —
2 Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
Et il n’écouta point, ni lui, ni ses serviteurs, ni le peuple du pays, les paroles que Yahweh avait prononcées par l’intermédiaire de Jérémie, le prophète.
3 Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
Le roi Sédécias envoya Juchal, fils de Sélémias, et Sophonie, fils de Maasias, le prêtre, vers Jérémie le prophète, pour lui dire: « Intercède donc pour nous auprès de Yahweh, notre Dieu. »
4 To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
Jérémie allait et venait au milieu du peuple, et on ne l’avait pas encore mis en prison.
5 Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
Or l’armée de Pharaon était sortie d’Égypte, et les Chaldéens qui assiégeaient Jérusalem, en ayant appris la nouvelle, s’étaient éloignés de Jérusalem.
6 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
Alors la parole de Yahweh fut adressée à Jérémie le prophète en ces termes:
7 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
Ainsi parle Yahweh, Dieu d’Israël: Vous parlerez ainsi au roi de Juda qui vous a envoyés pour m’interroger: Voici, l’armée de Pharaon qui est sortie pour vous secourir va retourner en son pays, en Égypte.
8 Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
Et les Chaldéens reviendront, et ils combattront contre cette ville; ils la prendront et la brûleront.
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
Ainsi parle Yahweh: Ne vous faites pas illusion en disant: Les Chaldéens s’en iront sûrement loin de nous. Car ils ne s’en iront pas.
10 Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
Et même quand vous auriez battu toute l’armée des Chaldéens qui combattent contre vous, et qu’il ne resterait d’eux que des blessés, ils se lèveraient chacun dans sa tente et brûleraient cette ville par le feu.
11 Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
Pendant que l’armée des Chaldéens s’était éloignée de Jérusalem, à cause de l’armée de Pharaon,
12 sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
Jérémie sortit de Jérusalem pour aller au pays de Benjamin, afin de retirer de là sa portion au milieu du peuple.
13 Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
Mais pendant qu’il était à la porte de Benjamin, le capitaine de la garde, nommé Jérias, fils de Sélémias, fils de Hananias, arrêta Jérémie le prophète, en disant: « Tu passes aux Chaldéens! »
14 Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
Jérémie répondit: « C’est, faux, je ne passe pas aux Chaldéens! » Mais Jérias ne l’écouta point; il arrêta Jérémie et l’amena aux chefs.
15 Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
Et les chefs s’emportèrent contre Jérémie; ils le battirent et le mirent en prison, dans la maison de Jonathan, le secrétaire; car ils en avaient fait une prison.
16 Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
Lorsque Jérémie eut pénétré dans la basse-fosse, sous les voûtes, et que Jérémie y fut resté bien des jours,
17 Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
Sédécias l’envoya tirer de là. Il l’interrogea secrètement dans sa maison, et lui dit: « Y a-t-il une parole de la part de Yahweh? » Et Jérémie répondit: « Oui! » et il ajouta: « Tu seras livré entre les mains du roi de Babylone. »
18 Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
Jérémie dit encore au roi Sédécias: « Quelle offense ai-je commise contre toi, contre tes serviteurs et contre ce peuple, que vous m’ayez mis en prison?
19 Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
Et où sont vos prophètes qui vous prophétisaient en disant: Le roi de Babylone ne viendra pas contre vous, ni contre ce pays?
20 Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
Et maintenant écoute, je te prie, ô roi, mon seigneur! Que ma supplication arrive devant toi: Ne me renvoie pas dans la maison de Jonathan, le secrétaire, pour y mourir. »
21 Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.
Le roi Sédécias donna l’ordre de garder Jérémie dans la cour de la prison et de lui donner chaque jour une miche de pain, de la rue des boulangers, jusqu’à ce que tout le pain fût consommé dans la ville. Ainsi Jérémie demeura dans la cour de la prison.