< Irmiya 37 >

1 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
And Zedekiah the son of Josiah reigned as king in the place of Conyahu the son of Jehoyakim, whom Nebuchadrezzar the king of Babylon made king in the land of Judah.
2 Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
But neither he, nor his servants, nor the people of the land, did hearken unto the words of the Lord, which he had spoken by means of Jeremiah the prophet.
3 Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
And king Zedekiah sent Jehuchal the son of Shelemyah and Zephanyahu the son of Ma'asseyah the priest unto Jeremiah the prophet, saying, Pray now in our behalf unto the Lord our God.
4 To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
Now Jeremiah came and went out among the people; and they put him not into the prison-house.
5 Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
But the army of Pharaoh was come forth out of Egypt: and when the Chaldeans that besieged Jerusalem heard the report of them, they withdrew from Jerusalem.
6 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
Then came the word of the Lord unto Jeremiah the prophet, saying,
7 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
Thus hath said the Lord, the God of Israel, Thus shall ye say to the king of Judah, that hath sent you unto me to inquire of me, Behold, Pharaoh's army, which is come forth to help you, returneth into its own land to Egypt.
8 Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
But the Chaldeans will come again, and fight against this city, and capture it, and burn it with fire.
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
Thus hath said the Lord, Deceive not yourselves, saying, The Chaldeans will certainly go away from us; for they will not go away.
10 Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
For if even ye had smitten the whole army of the Chaldeans that fight against you, and there remained among them [only such] men as are pierced through: yet should they rise up, every man in his tent, and burn this city with fire.
11 Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
And it came to pass, when the army of the Chaldeans had withdrawn from Jerusalem because of the army of Pharaoh,
12 sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
That Jeremiah went forth out of Jerusalem to go into the land of Benjamin, to make his escape thence in the midst of the people.
13 Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
But as he was in the gate of Benjamin, there was there a captain of the guardsmen, whose name was Yiriyah, the son of Shelemyah, the son of Chananyah; and he seized hold of Jeremiah the prophet, saying, Thou runnest away to the Chaldeans.
14 Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
But Jeremiah said, It is false; I am not running away to the Chaldeans. But he listened not to him; and Yiriyah seized hold of Jeremiah, and brought him to the princes.
15 Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
Thereupon were the princes wroth with Jeremiah, and struck him, and put him in prison in the house of Jonathan the scribe; for that had they made into a prison-house.
16 Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
When Jeremiah had been placed in the dungeon, within the traders' shops, where Jeremiah remained many days:
17 Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
King Zedekiah sent, and had him taken out, and the king asked him in his house in secret, and said, “Is there any word from the Lord?” And Jeremiah said, “There is:” and he said, Into the hand of the king of Babylon shalt thou be given up.
18 Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
And Jeremiah said unto king Zedekiah, What have I sinned against thee, and against thy servants, and against this people, that ye have put me into the prison-house?
19 Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
And where are now your prophets who have prophesied unto you, saying, The king of Babylon will not come against you, and against this land?
20 Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
Yet now, do but hear, I pray thee, O my lord the king: let me offer my humble supplication, I pray thee, before thee, that thou wilt not make me return to the house of Jonathan the scribe, lest I die there.
21 Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.
Then commanded king Zedekiah that they should put Jeremiah in ward in the court of the prison, and that they should give him a loaf of bread for every day out of the bakers' street, until all the bread was spent out of the city. Thus Jeremiah remained in the court of the prison.

< Irmiya 37 >