< Irmiya 37 >

1 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
Zedekias, Josias's Søn, blev Konge i Konjas, Jojakims Søns, Sted, idet Kong Nebukadrezar af Babel satte ham til Konge i Judas Land.
2 Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
Men han og hans Mænd og Landets Befolkning hørte ikke paa de Ord, HERREN talede ved Profeten Jeremias.
3 Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
Kong Zedekias sendte Jukal, Sjelemjas Søn, og Præsten Zefanja, Ma'asejas Søn, til Profeten Jeremias og lod sige: »Gaa i Forbøn for os hos HERREN vor Gud!«
4 To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
Dengang gik Jeremias frit ud og ind blandt Folket, thi man havde endnu ikke kastet ham i Fængsel.
5 Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
Faraos Hær var rykket ud fra Ægypten; og da Kaldæerne, som belejrede Jerusalem, fik Nys herom, var de brudt op fra Jerusalem.
6 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
Da kom HERRENS Ord til Profeten Jeremias saaledes:
7 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
Saa siger HERREN, Israels Gud: Saaledes skal du sige til Judas Konge, som har sendt Bud til dig for at raadspørge mig: Se, Faraos Hær, som er rykket ud for at hjælpe eder, skal vende hjem til Ægypten;
8 Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
og Kaldæerne skal vende tilbage og angribe denne By, indtage og afbrænde den.
9 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
Saa siger HERREN: Nar ikke eder selv ved at sige: »Kaldæerne drager bort fra os for Alvor!« Thi de drager ikke bort.
10 Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
Ja, om I saa slog hele Kaldæernes Hær, der angriber eder, saa der kun blev nogle saarede tilbage, hver i sit Telt, saa skulde de staa op og afbrænde denne By.
11 Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
Da Kaldæernes Hær var brudt op fra Jerusalem for Faraos Hær,
12 sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
gik Jeremias ud af Jerusalem for at drage til Benjamins Land og faa en Arvelod iblandt Befolkningen.
13 Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
Men da han kom til Benjaminsporten, var der en Vagthavende ved Navn Jir'ija, en Søn af Hananjas Søn Sjelemja, og han greb Profeten Jeremias og sagde: »Du vil løbe over til Kaldæerne.«
14 Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
Jeremias svarede: »Det er Løgn; jeg vil ikke løbe over til Kaldæerne.« Jir'ija vilde dog ikke høre ham, men greb ham og bragte ham til Fyrsterne;
15 Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
og Fyrsterne vrededes paa Jeremias, slog ham og lod ham bringe til Statsskriveren Jonatans Hus; thi det havde de gjort til Fængsel.
16 Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
Saaledes kom Jeremias i Fangehuset i Kælderen; og der sad han en Tid lang.
17 Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
Men Kong Zedekias sendte Bud og lod ham hente; og Kongen spurgte ham i al Hemmelighed i sit Palads: »Er der et Ord fra HERREN?« Jeremias svarede: »Ja, der er: Du skal overgives i Babels Konges Haand.«
18 Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
Derpaa sagde Jeremias til Kong Zedekias: »Hvad Synd har jeg gjort imod dig, dine Mænd og dette Folk, siden I har kastet mig i Fængsel?
19 Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
Og hvor er nu eders Profeter, som profeterede for eder, at Babels Konge ikke skulde komme over eder og dette Land?
20 Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
Saa hør da, Herre Konge! Lad min Bøn naa dig og lad mig ikke bringe tilbage til Statsskriveren Jonatans Hus, at jeg ikke skal dø der!«
21 Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.
Da bød Kong Zedekias, at man skulde holde Jeremias i Varetægt i Vagtforgaarden; og der gaves ham daglig et Stykke Brød fra Bagerens Gade, indtil Brødet slap op i Byen. Saaledes sad nu Jeremias i Vagtforgaarden.

< Irmiya 37 >