< Irmiya 36 >

1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
Pripetilo se je v četrtem letu Jojakíma, Jošíjevega sina, Judovega kralja, da je ta beseda prišla Jeremiju od Gospoda, rekoč:
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
»Vzemi zvitek knjige in zapiši vanjo vse besede, ki sem ti jih govoril zoper Izrael in zoper Juda in zoper vse narode, od dneva, ko sem ti spregovoril, od Jošíjevih dni, celo do tega dne.
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Morda bo Judova hiša prisluhnila vsemu zlu, ki jim ga nameravam storiti, da se bodo lahko vrnili vsak človek iz svoje zle poti, da bi lahko odpustil njihovo krivičnost in njihov greh.«
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
Potem je Jeremija poklical Nerijájevega sina Baruha in Baruh je iz Jeremijevih ust zapisal vse besede od Gospoda, ki mu jih je povedal, v zvitek knjige.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
Jeremija je zapovedal Baruhu, rekoč: »Jaz sem zaprt; ne morem iti v Gospodovo hišo.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
Zato pojdi ti in beri iz zvitka, ki si ga zapisal iz mojih ust, besede od Gospoda v ušesa ljudstva, v Gospodovi hiši, na dan posta, in bral jih boš tudi v ušesa vsega Juda, ki pride iz njihovih mest.
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Morda bodo predstavili svojo ponižno prošnjo pred Gospodom in se bodo vrnili vsak iz svoje zle poti, kajti velika je jeza in razjarjenost, ki jo je Gospod proglasil zoper to ljudstvo.«
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
Nerijájev sin Baruh je storil glede na vse, kar mu je prerok Jeremija zapovedal, ko je iz knjige bral besede od Gospoda v Gospodovi hiši.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
Pripetilo se je v petem letu Jojakíma, Jošíjevega sina, Judovega kralja, v devetem mesecu, da so razglasili post pred Gospodom vsemu ljudstvu v Jeruzalemu in vsemu ljudstvu, ki je iz Judovih mest prišlo v Jeruzalem.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
Potem je Baruh v knjigi bral Jeremijeve besede v Gospodovi hiši, v sobi Gemarjája, Šafánovega sina, pisarja, na višjem dvoru, ob vhodu novih velikih vrat Gospodove hiše, v ušesa vsega ljudstva.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
Ko je Mihajá, sin Gemarjája, sin Šafána, iz knjige slišal vse Gospodove besede,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
je potem odšel dol v kraljevo hišo, v pisarjevo sobo. Glej, vsi princi so sedeli tam, celó pisar Elišamá in Šemajájev sin Delajája in Ahbórjev sin Elnatána, Šafánov sin Gemarjá in Hananjájev sin Sedekíja in vsi princi.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
Potem jim je Mihajá naznanil vse besede, ki jih je slišal, ko je Baruh bral knjigo v ušesa ljudstva.
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
Zatorej so vsi princi k Baruhu poslali Jehudíja, sina Netanjája, sina Šelemjája, sina Kušíja, rekoč: »V svojo roko vzemi zvitek, ki si ga prebral v ušesa ljudstva in pridi.« Tako je Nerijájev sin Baruh vzel zvitek v svojo roko in prišel k njim.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
Rekli so mu: »Usedi se sedaj in preberi to v naša ušesa.« Tako je Baruh to prebral v njihova ušesa.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
Pripetilo se je torej, ko so slišali vse besede, da so bili prestrašeni, tako eni kakor drugi in rekli Baruhu: »Zagotovo bomo o vseh teh besedah povedali kralju.«
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
Baruha pa so vprašali, rekoč: »Sedaj nam povej: ›Kako si zapisal vse te besede pri njegovih ustih?‹«
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
Potem jim je Baruh odgovoril: »On mi je vse te besede proglasil s svojimi usti, jaz pa sem jih s črnilom zapisal v knjigo.«
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
Potem so princi rekli Baruhu: »Pojdi, skrij se, ti in Jeremija. Naj noben človek ne ve, kje sta.«
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
Vstopili so h kralju na dvor, toda zvitek so položili v sobo pisarja Elišamá in vse besede povedali kralju v ušesa.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
Tako je kralj poslal Jehudíja, da prinese zvitek in ta ga je vzel iz sobe pisarja Elišamája. In Jehudí ga je prebral v ušesa kralja in v ušesa vseh princev, ki so stali poleg kralja.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
Torej kralj je sedel v zimski hiši, v devetem mesecu in tam je bil ogenj, ki je pred njim gorel na ognjišču.
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
Pripetilo se je, da ko je Jehudí prebral tri ali štiri stolpce, je on to odrezal z nožkom in to vrgel v ogenj, ki je bil na ognjišču, dokler ni bil ves zvitek použit v ognju, ki je bil na ognjišču.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
Vendar niso bili prestrašeni, niti pretrgali svojih oblek niti kralj, niti katerikoli izmed njegovih služabnikov, ki so slišali vse te besede.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
Kljub temu so Elnatán, Delajá in Gemarjá posredovali h kralju, da ne bi zažgal zvitka, toda ni jih hotel poslušati.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
Toda kralj je zapovedal Jerahmeélu, sinu Hameleha in Serajáju, sinu Azriéla in Šelemjájevemu sinu Abdeélu, da primejo pisarja Baruha in preroka Jeremija, toda Gospod ju je skril.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Potem je Jeremiju prišla beseda od Gospoda, potem ko je kralj sežgal zvitek in besede, ki jih je Baruh zapisal pri Jeremijevih ustih, rekoč:
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
»Ponovno si vzemi drug zvitek in nanj zapiši vse prejšnje besede, ki so bile na prvem zvitku, ki ga je Judov kralj Jojakím sežgal.
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Judovemu kralju Jojakímu pa boš rekel: ›Tako govori Gospod: ›Ti si sežgal ta zvitek, rekoč: ›Zakaj si pisal tja noter, rekoč: ›Babilonski kralj bo zagotovo prišel in uničil to deželo in bo povzročil, da sta od tam odvzeta človek in žival?‹‹
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
Zato tako govori Gospod o Judovem kralju Jojakímu: ›Nikogar ne bo imel, da sedi na Davidovem prestolu, in njegovo truplo bo vrženo ven, podnevi v vročino in ponoči v zmrzal.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
Kaznoval ga bom, njegovo seme in njegove služabnike zaradi njihove krivičnosti in jaz bom privedel nadnje, nad prebivalce Jeruzalema in nad Judove može, vse zlo, ki sem ga proglasil zoper njih; toda niso mi prisluhnili.‹«
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
Potem je Jeremija vzel drug zvitek in ga izročil pisarju Baruhu, Nerijájevemu sinu, ki je iz Jeremijevih ust nanj zapisal vse besede iz knjige, ki jo je Judov kralj Jojakím sežgal v ognju. Poleg teh so jim bile dodane mnoge druge podobne besede.

< Irmiya 36 >