< Irmiya 36 >
1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
I Judas konge Jojakims, Josias' sønns fjerde år kom dette ord til Jeremias fra Herren:
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
Ta dig en bokrull og skriv i den alle de ord jeg har talt til dig om Israel og Juda og alle hedningefolkene fra den dag da jeg først talte til dig, fra Josias' dager og like til denne dag!
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Kanskje Judas hus vil merke sig all den ulykke jeg tenker å gjøre dem, så de kan vende om, hver fra sin onde vei, og jeg kan forlate dem deres misgjerning og deres synd.
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
Da kalte Jeremias til sig Baruk, Nerijas sønn, og Baruk skrev efter Jeremias' munn alle de ord som Herren hadde talt til ham, i en bokrull.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
Og Jeremias talte til Baruk og sa: Jeg er forhindret, jeg kan ikke komme til Herrens hus.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
Men gå du dit og les av rullen som du har skrevet efter min munn, Herrens ord op for folket i Herrens hus på en fastedag! Også for hele Juda, som kommer fra sine byer, skal du lese den.
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Kanskje de vil legge sin ydmyke bønn frem for Herrens åsyn og vende om, hver fra sin onde vei; for stor er den vrede og harme som Herren har uttalt over dette folk.
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
Og Baruk, Nerijas sønn, gjorde alt som profeten Jeremias hadde pålagt ham, og leste Herrens ord op av boken i Herrens hus.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
For i Judas konge Jojakims, Josias' sønns femte år, i den niende måned, blev det ropt ut at alt folket i Jerusalem og alt folket som var kommet fra Judas byer til Jerusalem, skulde faste for Herrens åsyn.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
Da leste Baruk op av boken Jeremias' ord i Herrens hus, i statsskriveren Gemarjas, Safans sønns kammer i den øvre forgård, ved inngangen til den nye port i Herrens hus, mens alt folket hørte på.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
Da Mikaja, sønn av Gemarja, sønn av Safan, hørte alle Herrens ord bli lest op av boken,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
gikk han ned til kongens hus, til statsskriverens kammer, og der fant han alle høvdingene sittende: statsskriveren Elisama og Delaja, Sjemajas sønn, og Elnatan, Akbors sønn, og Gemarja, Safans sønn, og Sedekias, Hananjas sønn, og alle de andre høvdinger.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
Og Mikaja fortalte dem om alle de ord han hadde hørt da Baruk leste op av boken for folket.
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
Da sendte alle høvdingene Jehudi, sønn av Netanja, sønn av Selemja, sønn av Kusi, til Baruk og sa: Ta med dig rullen som du leste op av for folket, og kom hit! Og Baruk, Nerijas sønn, tok rullen med sig og kom til dem.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
De sa til ham: Sett dig ned og les den for oss! Og Baruk leste den for dem.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
Og da de hørte alle ordene, vendte de sig forferdet til hverandre, og de sa til Baruk: Vi må melde kongen alt dette.
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
Så spurte de Baruk: Fortell oss hvorledes du skrev alle disse ord efter hans munn!
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
Baruk svarte: Med sin munn foresa han mig alle disse ord, og jeg skrev dem i boken med blekk.
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
Da sa høvdingene til Baruk: Gå og skjul dig, du og Jeremias, og la ingen vite hvor I er!
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
Så gikk de inn til kongen i forgården, men rullen la de ned i statsskriveren Elisamas kammer; og de fortalte alt dette til kongen.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
Da sendte kongen Jehudi avsted for å hente rullen, og han hentet den fra statsskriveren Elisamas kammer, og Jehudi leste den op for kongen og alle høvdingene som stod hos kongen.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
Kongen satt i vinterhuset, for det var den niende måned, og det brente ild i et fyrfat foran ham,
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
og da Jehudi hadde lest op tre eller fire blad, skar kongen rullen i stykker med en pennekniv og kastet den på ilden i fyrfatet, inntil hele rullen var fortært av ilden der i fyrfatet.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
Og de forferdedes ikke og sønderrev ikke sine klær, hverken kongen eller nogen av hans tjenere som hørte alle disse ord,
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
og skjønt Elnatan og Delaja og Gemarja inntrengende bad kongen at han ikke skulde brenne rullen, hørte han ikke på dem.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
Så bød kongen Jerahme'el, kongesønnen, og Seraja, Asriels sønn, og Selemja, Abde'els sønn, å gripe skriveren Baruk og profeten Jeremias; men Herren skjulte dem.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Da kom Herrens ord til Jeremias, efterat kongen hadde brent op rullen med de ord Baruk hadde skrevet efter Jeremias' munn:
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
Ta dig en annen rull og skriv i den alle de forrige ord, de som stod i den forrige rull, som Judas konge Jojakim brente op!
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Og om Judas konge Jojakim skal du si: Så sier Herren: Du brente denne rull og sa: Hvorfor skrev du i den således: Babels konge skal komme og ødelegge dette land og utrydde mennesker og dyr av det?
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
Derfor sier Herren så om Judas konge Jojakim: Han skal ikke ha nogen ætling som skal sitte på Davids trone, og hans døde kropp skal ligge slengt bort, utsatt for heten om dagen og for kulden om natten.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
Og jeg vil hjemsøke ham og hans ætt og hans tjenere for deres misgjerning, og jeg vil la komme over dem og over Jerusalems innbyggere og over Judas menn all den ulykke jeg har forkynt dem uten at de vilde høre.
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
Da tok Jeremias en annen rull og gav den til skriveren Baruk, Nerijas sønn, og han skrev i den efter Jeremias' munn alle ordene i den bok som Judas konge Jojakim hadde brent i ilden, og det blev til dem ennu lagt mange lignende ord.