< Irmiya 36 >

1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
Kwasekusithi ngomnyaka wesine kaJehoyakhimi, indodana kaJosiya, inkosi yakoJuda, lelilizwi lafika kuJeremiya livela eNkosini, lisithi:
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
Zithathele umqulu wogwalo, ubhale kiwo wonke amazwi engiwakhulume kuwe ngoIsrayeli langoJuda langazo zonke izizwe, kusukela ngosuku lokukhuluma kwami kuwe, kusukela ensukwini zikaJosiya, kuze kube lamuhla.
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Mhlawumbe abendlu kaJuda bazakuzwa bonke ububi engicabanga ukubenza kubo; ukuze baphenduke, ngulowo lalowo endleleni yakhe embi, ukuze ngithethelele ububi babo lesono sabo.
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
UJeremiya wasebiza uBharukhi indodana kaNeriya; uBharukhi wasebhala okuvela emlonyeni kaJeremiya, wonke amazwi eNkosi eyayiwakhulume kuye, emqulwini wogwalo.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
UJeremiya waselaya uBharukhi esithi: Ngivinjelwe, kangilakungena endlini yeNkosi.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
Ngakho hamba wena, ufunde emqulwini owubhalileyo, kuvela emlonyeni wami, amazwi eNkosi endlebeni zabantu endlini yeNkosi ngosuku lokuzila ukudla; uwafunde futhi endlebeni zakhe wonke uJuda abavela emizini yabo.
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Mhlawumbe ukuncenga kwabo kuzakuwa phambi kweNkosi, baphenduke, ngulowo lalowo endleleni yakhe embi; ngoba lukhulu ulaka lentukuthelo iNkosi ekukhulume kulababantu.
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
UBharukhi indodana kaNeriya wasesenza njengakho konke uJeremiya umprofethi ayemlaye khona, efunda egwalweni amazwi eNkosi endlini yeNkosi.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
Kwasekuthi emnyakeni wesihlanu kaJehoyakhimi, indodana kaJosiya, inkosi yakoJuda, ngenyanga yesificamunwemunye, bamemezela ukuzila ukudla phambi kweNkosi, bonke abantu eJerusalema, labantu bonke abavela emizini yakoJuda eJerusalema.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
UBharukhi wasefunda egwalweni amazwi kaJeremiya endlini yeNkosi, ekamelweni likaGemariya, indodana kaShafani, umbhali, egumeni elingaphezulu, emnyango wesango elitsha lendlu yeNkosi, endlebeni zabantu bonke.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
UMikhaya, indodana kaGemariya, indodana kaShafani, wasesizwa wonke amazwi eNkosi avela kulolugwalo,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
wehlela endlini yenkosi, ekamelweni lombhali; khangela-ke, zonke iziphathamandla zazihlezi lapho, uElishama umbhali, loDelaya indodana kaShemaya, loElinathani indodana kaAkhibhori, loGemariya indodana kaShafani, loZedekhiya indodana kaHananiya, leziphathamandla zonke.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
UMikhaya wasebatshela wonke amazwi ayewezwile, lapho uBharukhi efunda egwalweni endlebeni zabantu.
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
Zonke iziphathamandla zasezithuma uJehudi, indodana kaNethaniya, indodana kaShelemiya, indodana kaKushi, kuBharukhi, zisithi: Umqulu ofunde kuwo endlebeni zabantu, uthathe ngesandla sakho uze. Ngakho uBharukhi indodana kaNeriya wathatha umqulu ngesandla sakhe, waya kuzo.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
Zasezisithi kuye: Ake uhlale phansi, uwufunde endlebeni zethu. UBharukhi wasefunda endlebeni zazo.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
Kwasekusithi sezizwile wonke amazwi, zethukile, ngulowo lalowo ekhangele kumakhelwane wakhe, zathi kuBharukhi: Sizayitshela isibili inkosi wonke amazwi la.
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
Zasezimbuza uBharukhi zisithi: Ake usitshele, wawabhala njani wonke lamazwi emlonyeni wakhe?
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
UBharukhi wasesithi kuzo: Wangifundela wonke lamazwi evela emlonyeni wakhe, ngawabhala egwalweni ngeyinki.
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
Iziphathamandla zasezisithi kuBharukhi: Hamba ucatshe, wena loJeremiya, kakungabi lamuntu owaziyo lapho elikhona.
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
Zasezingena enkosini egumeni, kodwa umqulu zawubeka ekamelweni likaElishama umbhali; zakhuluma wonke amazwi endlebeni zenkosi.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
Inkosi yasithuma uJehudi ukuthi awulande umqulu; wasewuthatha ekamelweni likaElishama umbhali; uJehudi wawufunda endlebeni zenkosi lendlebeni zazo zonke iziphathamandla ezazimi enkosini.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
Inkosi yayihlezi-ke endlini yobusika ngenyanga yesificamunwemunye; umlilo wawuvutha embawuleni phambi kwayo.
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
Kwasekusithi lapho uJehudi esefundile amakhasi amathathu loba amane, yawasika ngengqamu yombhali, yawaphosela emlilweni osembawuleni, waze watsha waphela umqulu wonke emlilweni osembawuleni.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
Kodwa kabesabanga, kabadabulanga izembatho zabo, inkosi lenceku zayo zonke, abawezwayo wonke lamazwi.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
Loba kunjalo labo oElinathani loDelaya loGemariya beyincenga inkosi ukuthi ingawutshisi umqulu, kodwa kayibalalelanga.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
Kodwa inkosi yalaya uJerameli indodana yenkosi, loSeraya indodana kaAziriyeli, loShelemiya indodana kaAbideli, ukuze babambe uBharukhi umbhali loJeremiya umprofethi; kodwa iNkosi yabafihla.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Ilizwi leNkosi laselifika kuJeremiya emva kokuthi inkosi isiwutshisile umqulu lamazwi uBharukhi ayewabhalile evela emlonyeni kaJeremiya, lisithi:
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
Zithathele futhi omunye umqulu, ubhale kuwo wonke amazwi okuqala ayesemqulwini wokuqala, uJehoyakhimi inkosi yakoJuda eyawatshisayo.
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Njalo uzakuthi kuJehoyakhimi inkosi yakoJuda: Itsho njalo iNkosi: Wena utshisile lumqulu, usithi: Ubhaleleni kiwo usithi: Inkosi yeBhabhiloni izafika isibili, ilichithe lelilizwe, yenze ukuthi kuphele kulo abantu lenyamazana?
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
Ngakho itsho njalo iNkosi mayelana loJehoyakhimi inkosi yakoJuda: Kayikuba lamuntu ohlala esihlalweni sobukhosi sikaDavida; lesidumbu sakhe sizaphoselwa ekutshiseni kwemini lekuqandeni kobusuku.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
Ngizamjezisa-ke yena, lenzalo yakhe, lenceku zakhe, ububi babo; ngehlisele phezu kwabo laphezu kwabahlali beJerusalema laphezu kwabantu bakoJuda konke okubi engikukhulume kubo, kodwa kabalalelanga.
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
UJeremiya wasethatha omunye umqulu, wawunika uBharukhi, indodana kaNeriya, umbhali, owabhala kiwo okuvela emlonyeni kaJeremiya wonke amazwi ogwalo uJehoyakhimi inkosi yakoJuda eyalutshisayo ngomlilo; kwengezelelwa-ke kiwo amanye amazwi amanengi afanana lawo.

< Irmiya 36 >