< Irmiya 36 >
1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
Ngomnyaka wesine kaJehoyakhimi indodana kaJosiya inkosi yakoJuda ilizwi leli lafika kuJeremiya livela kuThixo, lisithi:
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
“Thatha umqulu ulobe kuwo wonke amazwi engawatsho kuwe ngo-Israyeli, uJuda lezinye zonke izizwe kusukela ngiqalisa ukukhuluma kuwe ekubuseni kukaJosiya kuze kube khathesi.
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Mhlawumbe lapho abantu bakoJuda besizwa ngawo wonke umonakalo engiceba ukuwehlisela phezu kwabo, omunye lomunye wabo uzaphenduka ezindleleni zakhe ezimbi; kulapho-ke ngizabathethelela ububi babo lezono zabo.”
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
Ngakho uJeremiya wabiza uBharukhi indodana kaNeriya. Kwathi uJeremiya ewatsho wonke amazwi ayekhulunywe nguThixo, uBharukhi ewaloba emqulwini.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
UJeremiya wasesithi kuBharukhi, “Mina ngivalelwe; ngingeke ngiye ethempelini likaThixo.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
Ngakho yana endlini kaThixo ngosuku lokuzila ukudla ubalele abantu amazwi kaThixo asemqulwini owawaloba ngikutshela. Abalele bonke abantu bakoJuda abangena bevela emadolobheni akibo.
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Engxenye bazaletha isicelo sabo phambi kukaThixo, omunye lomunye aphenduke ezindleleni zakhe ezimbi, ngoba intukuthelo lolaka okumenyezelwe kulababantu nguThixo kukhulu.”
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
UBharukhi indodana kaNeriya wenza konke ayekutshelwe nguJeremiya umphrofethi ukuba akwenze; ethempelini likaThixo wabala amazwi kaThixo emqulwini.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
Ngenyanga yesificamunwemunye yomnyaka wesihlanu kaJehoyakhimi indodana kaJosiya inkosi yakoJuda, kwamenyezelwa isikhathi sokuzila ukudla phambi kukaThixo ebantwini bonke baseJerusalema lakulaba ababeze bevela emadolobheni akoJuda.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
Esendlini kaGemariya indodana kaShafani umabhalani, eyayisegumeni langaphezulu ekungeneni kweSango eLitsha lethempeli, uBharukhi wawabalela abantu bonke ethempelini likaThixo amazwi kaJeremiya asemqulwini.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
Kwathi uMikhaya indodana kaGemariya, indodana kaShafani, esezwe wonke amazwi kaThixo ayesemqulwini,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
waya phansi endlini kamabhalani esigodlweni, lapho izikhulu zonke ezazihlezi khona: u-Elishama umabhalani, uDelaya indodana kaShemaya, u-Elinathani indodana ka-Akhibhori, uGemariya indodana kaShafani, uZedekhiya indodana kaHananiya kanye lezinye zonke izikhulu.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
Emva kokuba uMikhaya esebatshele konke ayezwe uBharukhi ekubalela abantu emqulwini,
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
izikhulu zonke zathuma uJehudi indodana kaNethaniya, indodana kaShelemiya, indodana kaKhushi, ukuba ayekuthi kuBharukhi, “Woza lomqulu owubalele abantu.” Ngakho uBharukhi indodana kaNeriya waya kubo lomqulu ewuphethe ngesandla.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
Bathi kuye, “Ake uhlale phansi usibalele wona.” Ngakho uBharukhi wababalela.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
Sebezwe wonke amazwi la bakhangelana ngokwesaba, basebesithi kuBharukhi, “Amazwi la kumele siwabike wonke enkosini.”
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
Babuya bambuza uBharukhi bathi, “Sitshele, kwenzakale njani ukuthi ubhale konke lokhu? Kukhulunywe nguJeremiya na?”
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
UBharukhi waphendula wathi, “Ye, amazwi wonke la uwakhulume kimi, mina ngawaloba nge-inki emqulwini.”
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
Izikhulu zasezisithi kuBharukhi, “Wena loJeremiya hambani liyecatsha. Lingatsheli muntu ukuthi lingaphi.”
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
Sebefake umqulu endlini ka-Elishama umabhalani, baya enkosini egumeni bayibikela konke,
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
inkosi yathuma uJehudi ukuba ayethatha umqulu lowo, uJehudi weza lawo ewuthethe endlini ka-Elishama umabhalani wawubalela inkosi lezikhulu zonke ezazimi phansi kwayo.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
Kwakuyinyanga yesificamunwemunye, njalo inkosi yayihlezi ekamelweni lebusika, kulomlilo ovuthayo eziko phambi kwayo.
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
Kwakusithi uJehudi angabala izigaba ezintathu loba ezine zomqulu, inkosi iziqume ngengqamu iziphosele eziko umqulu waze watsha wonke emlilweni.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
Inkosi lezinceku zayo zonke ezawezwayo amazwi la kabesabanga loba badabule izigqoko zabo.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
Lanxa u-Elinathani loDelaya kanye loGemariya bayincenga inkosi ukuba ingatshisi umqulu, kayibalalelanga.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
Esikhundleni salokho inkosi yalaya uJerameli, indodana yenkosi, loSeraya indodana ka-Aziriyeli kanye loShelemiya indodana ka-Abhideli ukuba babophe uBharukhi umbhali kanye loJeremiya umphrofethi. Kodwa uThixo wayesebafihlile.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Inkosi isitshise umqulu owawulamazwi ayebhalwe nguBharukhi ewatshelwa nguJeremiya, ilizwi likaThixo lafika kuJeremiya lisithi,
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
“Thatha omunye umqulu ulobe kuwo wonke amazwi abesemqulwini wakuqala, otshiswe nguJehoyakhimi inkosi yakoJuda.
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Umtshele uJehoyakhimi inkosi yakoJuda uthi, ‘UThixo uthi: Utshise umqulu lowana wathi, “Kungani ulobe kuwo ukuthi inkosi yaseBhabhiloni izakuza ngempela ichithe ilizwe leli, iqothule abantu lezinyamazana kulo na?”
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
Ngakho mayelana loJehoyakhimi inkosi yakoJuda, uThixo uthi: Akayikuba lomuntu ozahlala esihlalweni sobukhosi sikaDavida; isidumbu sakhe sizaphoselwa phandle sichayeke ekutshiseni kwelanga lakungqwaqwane webusuku.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
Ngizamjezisa labantwana bakhe kanye lezinceku zakhe ngenxa yobubi babo. Ngizakwehlisela phezu kwabo laphezu kwalabo abahlala eJerusalema kanye labantu bakoJuda, wonke umonakalo engawumemezela kubo, ngoba kabalalelanga.’”
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
Ngakho uJeremiya wathatha omunye umqulu wawunika umbhali uBharukhi indodana kaNeriya, njalo kwathi uJeremiya emtshela uBharukhi waloba kuwo wonke amazwi omqulu owawutshiswe emlilweni nguJehoyakhimi inkosi yakoJuda. Kwengezelelwa ngamanye amazwi amanengi ayefana lalawo.