< Irmiya 36 >

1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
Et il arriva dans la quatrième année de Joakim, fils de Josias, roi de Juda, que cette parole fut adressée à Jérémie par le Seigneur, disant:
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
Prends un rouleau de livre et tu y écriras toutes les paroles que je t’ai dites contre Israël, et contre Juda, et contre tous les peuples, depuis le jour où je t’ai parlé, depuis les jours de Josias, jusqu’à ce jour;
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Pour voir si par hasard, la maison de Juda apprenant tous les maux que moi je pense leur faire, chacun reviendra de ses voies très mauvaises; et je lui pardonnerai son iniquité et son péché.
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
Jérémie appela donc Baruch, fils de Nérias, et Baruch écrivit, sorties de la bouche de Jérémie sur un rouleau de livre, toutes les paroles que le Seigneur lui avait dites.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
Et Jérémie ordonna à Baruch, disant: Moi je suis enfermé, et je ne puis entrer dans la maison du Seigneur.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
Entre donc, toi, et lis d’après le rouleau dans lequel tu as écrit, sorties de ma bouche, les paroles du Seigneur, le peuple entendant dans la maison du Seigneur, au jour de jeûne; de plus tous ceux de Juda qui viennent de leurs cités entendant, tu les leur liras;
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Pour voir si par hasard leur prière tombera devant le Seigneur, et s’ils reviendront chacun de sa voie très mauvaise; parce que grande est la fureur et l’indignation avec laquelle a parlé le Seigneur contre son peuple.
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
Et Baruch, fils de Nérias, fit selon tout ce que lui avait ordonné Jérémie, le prophète, lisant dans le rouleau les paroles du Seigneur, dans la maison du Seigneur.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
Or il arriva en la cinquième année de Joakim, fils de Josias, roi de Juda, dans le neuvième mois, qu’on publia un jeûne en présence du Seigneur, pour tout le peuple dans Jérusalem et pour toute la multitude qui avait afflué des cités de Juda dans Jérusalem.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
Et Baruch lut dans le rouleau les paroles de Jérémie dans la maison du Seigneur, dans la chambre du trésor de Gamarias, fils de Saphan, le scribe, dans le vestibule supérieur, à l’entrée de la porte neuve de la maison du Seigneur, tout le peuple entendant.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
Et lorsque Michée, fils de Gamarias, fils de Saphan, eut entendu toutes les paroles du Seigneur écrites dans le livre,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
Il descendit dans la maison du roi, en la chambre du trésor du scribe; et voilà que là tous les princes étaient assis: Elisama le Scribe, et Dalaïas, fils de Séméias, et Elnathan, fils d’Achobor, et Gamarias, fils de Saphan, et Sédécias, fils d’Hananias, et tous les princes.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
Et Michée leur rapporta toutes les paroles qu’il avait entendues de Baruch, lisant dans le rouleau aux oreilles du peuple.
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
C’est pourquoi tous les princes envoyèrent à Baruch Judi, fils de Nathanias, fils de Sélémias, fils de Chusi, disant: Prends en ta main le rouleau que tu as lu, le peuple entendant, et viens. Baruch, fils de Nérias, prit donc le rouleau en sa main, et vint à eux.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
Et ils lui dirent: Assieds-toi, et lis ces choses à nos oreilles. Et Baruch lut à leurs oreilles.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
Ainsi, lorsqu’ils eurent entendu toutes les paroles, ils se regardèrent les uns les autres avec étonnement, et ils dirent à Baruch: Nous devons rapporter au roi toutes ces paroles.
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
Et ils l’interrogèrent, disant: Déclare-nous comment tu as écrit toutes ces paroles sorties de la bouche de Jérémie.
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
Or Baruch leur dit: Il me disait de sa bouche toutes ces paroles comme s’il les avait lues; et moi je les écrivais dans le rouleau avec de l’encre.
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
Et les princes dirent à Baruch: Va, et cache-toi, ainsi que Jérémie, et que personne ne sache où vous serez.
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
Et ils entrèrent chez le roi dans le vestibule; quant au rouleau, ils l’avaient déposé dans la chambre du trésor d’Elisama, le scribe, et ils rapportèrent, le roi entendant, toutes les paroles.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
Et le roi envoya Judi afin de prendre le rouleau; lequel l’ayant pris de la chambre du trésor d’Elisama, le scribe, le lut, le roi entendant, ainsi que tous les princes qui étaient autour du roi.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
Or le roi était assis dans sa maison d’hiver au neuvième mois; et un brasier était placé devant lui, plein de charbons ardents.
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
Lorsque Judi eut lu trois ou quatre pages, le roi coupa le rouleau avec le canif du scribe, et le jeta dans le feu qui était sur le brasier, jusqu’à ce que le volume entier fût consumé par le feu qui était dans le brasier.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
Et le roi et tous ses serviteurs qui entendirent toutes ces paroles, ne craignirent pas, et ne déchirèrent pas leurs vêtements.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
Mais cependant Elnathan et Dalaïas et Gamarias, s’opposèrent au roi, afin qu’il ne brûlât point le livre; et il ne les écouta point.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
Et le roi ordonna à Jérémiel, fils d’Amélech, et à Saraïas, fils d’Ezriel, et à Sélémias, fils d’Abdéel, de prendre Baruch, le scribe, et Jérémie, le prophète; mais le Seigneur les cacha.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie, le prophète, après que le roi eut brûlé le rouleau et les paroles que Baruch avait écrites et qui étaient sorties de la bouche de Jérémie, disant:
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
Reprends un autre rouleau, et écris-y toutes les paroles qui étaient dans le premier rouleau qu’a brûlé Joakim, roi de Juda.
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Et à Joakim, roi de Juda, tu diras: Voici ce que dit le Seigneur: Tu as brûlé ce rouleau, disant: Pourquoi as-tu écrit dans ce livre en publiant: Soudain viendra le roi de Babylone, et il dévastera cette terre et il en fera disparaître l’homme et la bête?
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur contre Joakim, roi de Juda: Il n’y aura pas de lui de prince qui s’assiéra sur le trône de David; et son cadavre sera jeté à la chaleur du jour et à la gelée de la nuit.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
Et je visiterai contre lui, et contre sa race, et contre ses serviteurs, leurs iniquités; et j’amènerai sur eux et sur les habitants de Jérusalem et sur les hommes de Juda tout le mal que je leur ai annoncé, et ils ne m’ont pas entendu.
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
Or Jérémie prit un autre rouleau et le donna à Baruch, fils de Nérias, le scribe, qui y écrivit, sorties de la bouche de Jérémie, toutes les paroles qui étaient dans le livre qu’avait brûlé Joakim, roi de Juda; et il y ajouta en outre beaucoup plus de paroles qu’il n’y en avait auparavant.

< Irmiya 36 >