< Irmiya 36 >
1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
La quatrième année de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda, cette parole fut adressée à Jérémie de la part de Yahvé, en ces termes:
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
« Prends un rouleau de livre, et écris-y toutes les paroles que je t'ai dites contre Israël, contre Juda et contre toutes les nations, depuis le jour où je t'ai parlé, depuis l'époque de Josias jusqu'à ce jour.
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Peut-être la maison de Juda entendra-t-elle tout le mal que j'ai l'intention de lui faire, afin que chacun revienne de sa mauvaise voie, et que je pardonne son iniquité et son péché. »
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
Jérémie appela Baruc, fils de Neriah, et Baruc écrivit de la bouche de Jérémie toutes les paroles de l'Éternel, qu'il lui avait dites, sur un rouleau de livre.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
Jérémie donna un ordre à Baruc, en disant: « Je suis limité. Je ne peux pas entrer dans la maison de Yahvé.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
Va donc, et lis dans le rouleau que tu as écrit de ma bouche, les paroles de l'Éternel, aux oreilles du peuple dans la maison de l'Éternel, le jour du jeûne. Tu les liras aussi aux oreilles de tous les Judéens qui sortiront de leurs villes.
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Il se peut qu'ils présentent leurs supplications à l'Éternel et que chacun revienne de sa mauvaise voie, car l'Éternel a annoncé une grande colère et une grande fureur contre ce peuple. »
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
Baruc, fils de Nérija, fit tout ce que lui avait ordonné Jérémie, le prophète, en lisant dans le livre les paroles de l'Éternel, dans la maison de l'Éternel.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
Or, la cinquième année de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda, au neuvième mois, tout le peuple de Jérusalem et tout le peuple venu des villes de Juda à Jérusalem, proclamèrent un jeûne devant Yahvé.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
Et Baruch lut les paroles de Jérémie tirées du livre dans la maison de l'Éternel, dans la chambre de Gemaria, fils de Shaphan, le scribe, dans le parvis supérieur, à l'entrée de la nouvelle porte de la maison de l'Éternel, aux oreilles de tout le peuple.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
Lorsque Michée, fils de Guemaria, fils de Shaphan, eut entendu du livre toutes les paroles de l'Éternel,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
il descendit dans la maison du roi, dans la chambre du secrétaire; et voici, tous les princes étaient assis là, Élischama, le secrétaire, Delaja, fils de Schemaeja, Elnathan, fils d'Acbor, Guemaria, fils de Shaphan, Sédécias, fils de Hanania, et tous les princes.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
Et Michée leur rapporta toutes les paroles qu'il avait entendues, lorsque Baruch lisait le livre aux oreilles du peuple.
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
Alors tous les chefs envoyèrent Jehudi, fils de Nethania, fils de Shelemia, fils de Cushi, vers Baruch, en disant: « Prends en main le rouleau que tu as lu aux oreilles du peuple, et viens. » Baruch, fils de Neriah, prit le rouleau dans sa main et vint vers eux.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
Ils lui dirent: « Assieds-toi maintenant, et lis-le à notre intention. » Alors Baruch l'a lu à leur oreille.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
Or, lorsqu'ils eurent entendu toutes ces paroles, ils se tournèrent avec crainte les uns vers les autres, et dirent à Baruc:
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
« Ils demandèrent à Baruc: « Dis-nous maintenant comment tu as écrit toutes ces paroles à sa bouche? ».
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
Baruch leur répondit: « Il m'a dicté toutes ces paroles de sa bouche, et je les ai écrites avec de l'encre dans le livre. »
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
Alors les princes dirent à Baruch: « Toi et Jérémie, allez vous cacher. Que personne ne sache où vous êtes. »
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
Ils se rendirent auprès du roi dans la cour, mais ils avaient déposé le rouleau dans la chambre d'Elishama, le scribe. Ils racontèrent alors toutes ces paroles à l'oreille du roi.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
Le roi envoya Jehudi chercher le rouleau, et il le sortit de la chambre d'Elishama, le scribe. Jehudi le lut en présence du roi et de tous les princes qui se tenaient près du roi.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
Le roi était assis dans la maison d'hiver, au neuvième mois, et le feu brûlait devant lui dans le brasero.
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
Lorsque Jehudi eut lu trois ou quatre colonnes, le roi les coupa avec le canif et les jeta dans le feu qui était dans le brasier, jusqu'à ce que tout le rouleau fût consumé dans le feu qui était dans le brasier.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
Le roi et ses serviteurs, qui entendirent toutes ces paroles, n'eurent pas peur et ne déchirèrent pas leurs vêtements.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
Elnathan, Delaja et Gemaria avaient fait des instances auprès du roi pour qu'il ne brûle pas le rouleau, mais il ne voulut pas les écouter.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
Le roi ordonna à Jerahmeel, fils du roi, à Seraja, fils d'Azriel, et à Shelemiah, fils d'Abdeel, d'arrêter Baruch, le scribe, et Jérémie, le prophète; mais Yahvé les cacha.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
La parole de Yahvé fut adressée à Jérémie, après que le roi eut brûlé le rouleau et les paroles que Baruc écrivit à la bouche de Jérémie, en ces termes:
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
« Prends encore un autre rouleau, et écris-y toutes les paroles antérieures qui étaient dans le premier rouleau, que Jojakim, roi de Juda, a brûlé.
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Tu diras à propos de Jojakim, roi de Juda: « Yahvé dit: Tu as brûlé ce rouleau, en disant: Pourquoi as-tu écrit: Le roi de Babylone viendra certainement détruire ce pays, et il en fera disparaître les hommes et les bêtes?
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
C'est pourquoi Yahvé dit à propos de Jehoïakim, roi de Juda: « Il n'y aura personne pour s'asseoir sur le trône de David. Son cadavre sera jeté dehors, le jour à la chaleur, la nuit au gel.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
Je le punirai, lui, sa progéniture et ses serviteurs, pour leur iniquité. Je ferai venir sur eux, sur les habitants de Jérusalem et sur les hommes de Juda, tous les malheurs que j'ai prononcés contre eux, mais ils n'ont pas écouté. »'"
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
Jérémie prit un autre rouleau, et le donna à Baruc, le scribe, fils de Neriah, qui y écrivit de la bouche de Jérémie toutes les paroles du livre que Jojakim, roi de Juda, avait brûlé au feu, et beaucoup de paroles semblables y furent ajoutées.