< Irmiya 36 >
1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
And it was in the year fourth of Jehoiakim [the] son of Josiah [the] king of Judah it came the word this to Jeremiah from with Yahweh saying.
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
Take for yourself a scroll of a document and you will write to it all the words which I have spoken to you on Israel and on Judah and on all the nations from [the] day [when] I spoke to you from [the] days of Josiah and until the day this.
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Perhaps they will hear [the] house of Judah all the harm which I [am] planning to do to them so that they may turn back everyone from way his evil and I will forgive iniquity their and sin their.
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
And he called Jeremiah Baruch [the] son of Neriah and he wrote Baruch from [the] mouth of Jeremiah all [the] words of Yahweh which he had spoken to him on a scroll of a document.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
And he commanded Jeremiah Baruch saying I [am] shut up not I am able to go [the] house of Yahweh.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
And you will go you and you will read aloud in the scroll which you have written from mouth my [the] words of Yahweh in [the] ears of the people [the] house of Yahweh on a day of fasting and also in [the] ears of all Judah who are coming from cities their you will read aloud them.
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Perhaps it will fall supplication their before Yahweh so they may turn back everyone from way his evil for [is] great the anger and the rage which he has spoken Yahweh against the people this.
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
And he did Baruch [the] son of Neriah according to all that he had commanded him Jeremiah the prophet to read aloud in the scroll [the] words of Yahweh [the] house of Yahweh.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
And it was in the year fifth of Jehoiakim [the] son of Josiah [the] king of Judah in the month ninth they proclaimed a fast before Yahweh all the people in Jerusalem and all the people who were coming from [the] cities of Judah in Jerusalem.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
And he read aloud Baruch in the scroll [the] words of Jeremiah [the] house of Yahweh in [the] room of Gemariah [the] son of Shaphan the scribe in the court upper [the] entrance of [the] gate of [the] house of Yahweh new in [the] ears of all the people.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
And he heard Micaiah [the] son of Gemariah [the] son of Shaphan all [the] words of Yahweh from on the scroll.
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
And he went down [the] house of the king to [the] room of the scribe and there! there all the officials [were] sitting Elishama the scribe and Delaiah [the] son of Shemaiah and Elnathan [the] son of Achbor and Gemariah [the] son of Shaphan and Zedekiah [the] son of Hananiah and all the officials.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
And he told to them Micaiah all the words which he had heard when read aloud Baruch in the scroll in [the] ears of the people.
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
And they sent all the officials to Baruch Jehudi [the] son of Nethaniah [the] son of Shelemiah [the] son of Cushi saying the scroll which you have read aloud in it in [the] ears of the people take it in hand your and come and he took Baruch [the] son of Neriah the scroll in hand his and he went to them.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
And they said to him sit please and read aloud it in ears our and he read [it] aloud Baruch in ears their.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
And it was when heard they all the words they were in dread each to neighbor his and they said to Baruch certainly we will tell to the king all the things these.
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
And Baruch they asked saying tell please to us how? did you write all the words these from mouth his.
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
And he said to them Baruch from mouth his he proclaimed to me all the words these and I [was] writing on the scroll with ink.
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
And they said the officials to Baruch go hide yourself you and Jeremiah and anyone may not he know where? [are] you.
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
And they went to the king [the] court towards and the scroll they had deposited in [the] room of Elishama the scribe and they told in [the] ears of the king all the things.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
And he sent the king Jehudi to fetch the scroll and he fetched it from [the] room of Elishama the scribe and he read aloud it Jehudi in [the] ears of the king and in [the] ears of all the officials who were standing from with the king.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
And the king [was] sitting [the] house of the winter in the month ninth and the fire-pot before him [was] kindled.
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
And it was - when read aloud Jehudi three doors and four he tore it with [the] knife of the scribe and he threw [it] into the fire which [was] to the fire-pot until was consumed all the scroll on the fire which [was] on the fire-pot.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
And not they were afraid and not they tore clothes their the king and all servants his who heard all the words these.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
And also Elnathan and Delaiah and Gemariah they had made entreaty with the king to not to burn the scroll and not he listened to them.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
And he commanded the king Jerahmeel [the] son of the king and Seraiah [the] son of Azriel and Shelemiah [the] son of Abdeel to seize Baruch the scribe and Jeremiah the prophet and he hid them Yahweh.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
And it came [the] word of Yahweh to Jeremiah after - burned the king the scroll and the words which he had written Baruch from [the] mouth of Jeremiah saying.
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
Return take for yourself a scroll another and write on it all the words former which they were on the scroll former which he burned Jehoiakim [the] king of Judah.
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
And to Jehoiakim [the] king of Judah (you will say *LA(bh)*) thus he says Yahweh you you burned the scroll this saying why? did you write on it saying certainly he will come [the] king of Babylon and he will destroy the land this and he will cause to cease from it human being and animal.
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
Therefore thus he says Yahweh on Jehoiakim [the] king of Judah not he will belong to him [one who] sits on [the] throne of David and corpse his it will be thrown out to the heat in the day and to the frost in the night.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
And I will visit on him and on offspring his and on servants his iniquity their and I will bring on them and on [the] inhabitants of Jerusalem and to everyone of Judah all the calamity which I have spoken against them and not they listened.
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
And Jeremiah he took - a scroll another and he gave it to Baruch [the] son of Neriah the scribe and he wrote on it from [the] mouth of Jeremiah all [the] words of the scroll which he had burned Jehoiakim [the] king of Judah in the fire and again it was added to them words many like them.