< Irmiya 36 >
1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
And it comes to pass, in the fourth year of Jehoiakim son of Josiah king of Judah, this word has been to Jeremiah from YHWH, saying,
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
“Take a roll of a scroll to yourself, and you have written on it all the words that I have spoken to you concerning Israel, and concerning Judah, and concerning all the nations, from the day I spoke to you, from the days of Josiah, even to this day;
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
perhaps the house of Israel so hears all the evil that I am thinking of doing to them, so that they each turn back from his evil way, and I have been propitious to their iniquity, and to their sin.”
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
And Jeremiah calls Baruch son of Neriah, and Baruch writes from the mouth of Jeremiah all the words of YHWH, that He has spoken to him, on a roll of a scroll.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
And Jeremiah commands Baruch, saying, “I am restrained, I am not able to enter the house of YHWH;
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
but you have entered—and you have read in the scroll that you have written from my mouth, the words of YHWH, in the ears of the people, in the house of YHWH, in the day of the fast, and you also read them in the ears of all Judah who are coming in from their cities;
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
perhaps their supplication so falls before YHWH, and they each turn back from his evil way, for the anger and the fury that YHWH has spoken concerning this people [is] great.”
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
And Baruch son of Neriah does according to all that Jeremiah the prophet commanded him, to read in the scroll the words of YHWH in the house of YHWH.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
And it comes to pass, in the fifth year of Jehoiakim son of Josiah king of Judah, in the ninth month, they proclaimed a fast before YHWH to all the people in Jerusalem, and to all the people who are coming in from cities of Judah to Jerusalem;
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
and Baruch reads in the scroll the words of Jeremiah in the house of YHWH, in the chamber of Gemariah son of Shaphan the scribe, in the higher court, at the opening of the New Gate of the house of YHWH, in the ears of all the people.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
And Michaiah son of Gemariah, son of Shaphan, hears all the words of YHWH from off the scroll,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
and he goes down [to] the house of the king, to the chamber of the scribe, and behold, there all the heads are sitting: Elishama the scribe, and Delaiah son of Shemaiah, and Elnathan son of Acbor, and Gemariah son of Shaphan, and Zedekiah son of Hananiah, and all the heads.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
And Micaiah declares to them all the words that he has heard when Baruch reads in the scroll in the ears of the people;
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
and all the heads send to Baruch, Jehudi son of Nethaniah, son of Shelemiah, son of Cushi, saying, “Take in your hand the scroll, which you have read in the ears of the people, and come.” And Baruch son of Neriah takes the scroll in his hand and comes to them,
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
and they say to him, “Please sit down and read it in our ears,” and Baruch reads [it] in their ears,
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
and it comes to pass, when they hear all the words, they have been afraid—one to another—and say to Baruch, “We surely declare all these words to the king.”
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
And they asked Baruch, saying, “Please declare to us, how did you write all these words from his mouth?”
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
And Baruch says to them, “He pronounces from his mouth all these words to me, and I am writing on the scroll with ink.”
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
And the heads say to Baruch, “Go, be hidden, you and Jeremiah, and let no one know where you [are].”
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
And they go to the king, to the court, and they have laid up the scroll in the chamber of Elishama the scribe, and they declare all the words in the ears of the king.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
And the king sends Jehudi to take the scroll, and he takes it out of the chamber of Elishama the scribe, and Jehudi reads it in the ears of the king, and in the ears of all the heads who are standing by the king;
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
and the king is sitting in the winter-house, in the ninth month, and the stove is burning before him,
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
and it comes to pass, when Jehudi reads three or four leaves, he cuts it out with the scribe’s knife, and has cast [it] into the fire that [is] on the stove, until the consumption of all the scroll by the fire that [is] on the stove.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
And the king and all his servants who are hearing all these words have not been afraid, nor torn their garments.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
And also Elnathan, and Delaiah, and Gemariah have interceded with the king not to burn the scroll, and he has not listened to them.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
And the king commands Jerahmeel son of Hammelek, and Seraiah son of Azriel, and Shelemiah son of Abdeel, to take Baruch the scribe and Jeremiah the prophet, and YHWH hides them.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
And there is a word of YHWH to Jeremiah—after the king’s burning the scroll, even the words that Baruch has written from the mouth of Jeremiah—saying:
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
“Turn, take another scroll to yourself, and write on it all the former words that were on the first scroll that Jehoiakim king of Judah burned,
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
and say to Jehoiakim king of Judah, Thus said YHWH: You have burned this scroll, saying, Why have you written on it, saying, The king of Babylon surely comes in, and has destroyed this land, and caused man and beast to cease from it?
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
Therefore, thus said YHWH concerning Jehoiakim king of Judah: He has none sitting on the throne of David, and his carcass is cast out to heat by day, and to cold by night;
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
and I have charged on him, and on his seed, and on his servants, their iniquity; and I have brought in on them, and on the inhabitants of Jerusalem, and to the men of Judah, all the evil that I have spoken to them, and they did not listen.”
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
And Jeremiah has taken another scroll, and gives it to Baruch son of Neriah the scribe, and he writes on it from the mouth of Jeremiah all the words of the scroll that Jehoiakim king of Judah has burned in the fire; and again there were added to them many words like these.