< Irmiya 36 >
1 A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
E higa mar angʼwen mar Jehoyakim wuod Josia ruodh Juda, wachni nobiro ne Jeremia koa ir Jehova Nyasaye:
2 “Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
“Kaw kitabu kendo indikie weche duto ma asewacho kuom Israel gi Juda kod ogendini mamoko duto kochakore kinde mane achako wuoyo kodi e ndalo loch Josia nyaka sani.
3 Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
Sa moro ka jo-Juda owinjo kuom masichegi ma achano mar kelo kuomgi, to giduto ginilokre giwe yoregi mamono; eka anawenegi timbegi mamono kod richo mag-gi.”
4 Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
Omiyo Jeremia noluongo Baruk wuod Neria, kendo Jeremia ne wachone to ondiko weche duto mane Jehova Nyasaye osewachone, Baruk nondikogi e kitabu.
5 Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
Eka Jeremia nokone Baruk niya, “An otama; ok anyal dhi e hekalu mar Jehova Nyasaye.
6 Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
Omiyo in dhi e od Jehova Nyasaye chiengʼ lamo gi tweyo chiemo kendo isomne ji koa e kitabuni weche Jehova Nyasaye mane indiko sa mane awachoni to indiko. Somnegi ne jo-Juda duto ma biro koa e miechgi.
7 Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
Sa moro ginikel kwayogi e nyim Jehova Nyasaye, kendo giduto gilokre giwe yoregi mamono, nimar ich wangʼ gi mirima mikelone jogi gi Jehova Nyasaye duongʼ.”
8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
Baruk wuod Neria notimo gik moko duto mane Jeremia janabi onyise mondo otim; e hekalu mar Jehova Nyasaye nosomo weche Jehova Nyasaye koa e kitabu.
9 A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
E dwe mar ochiko e higa mar abich mar loch Jehoyakim wuod Josia ruodh Juda, kinde mar tweyo e nyim Jehova Nyasaye nolandne ji duto manie Jerusalem kod jogo mane obiro koa e dala mag Juda.
10 Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
Kochakore e agola mar Gemaria wuod Shafan ma jagoro, mane nitiere e laru man malo e kar donjo mar Dhorangach Manyien mar hekalu, Baruk nosomone ji duto e hekalu mar Jehova Nyasaye weche Jeremia koa e kitabu.
11 Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
Ka Mikaya wuod Gemaria, ma wuod Shafan, nowinjo weche duto mag Jehova Nyasaye moa e kitabu,
12 sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
nodhi e agola mar jagoro mane ni e kar dak ruoth, kama ne jotelo nobetie: Elishama ma jagoro, Delaya wuod Shemaya, Elnathan wuod Akbor, Gemaria wuod Shafan, Zedekia wuod Hanania, kod jotelo mamoko duto.
13 Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
Bangʼ ka Mikaya ne osenyisogi gik moko duto mane osewinjo ka Baruk somo ne ji koa e kitabu,
14 sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
jotelogi duto nooro Jehudi wuod Nethania, ma wuod Shelemia, wuod Kushi, mondo owach ne Baruk niya, “Kel kitabu ma isesomone ji kendo ibi.” Omiyo Baruk wuod Neria nodhi irgi gi kitabuno e lwete.
15 Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
Negiwachone, “Bed piny, kiyie, kendo isomnwago.” Omiyo Baruk nosomonegi.
16 Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
Kane gi winjo wechegi duto, ne gingʼiyore giwegi ka giluor kendo giwachone Baruk niya, “Nyaka wanyis wechegi duto ne ruoth.”
17 Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
Eka negipenjo Baruk niya, “Nyiswane, ere kaka ne indiko gigi duto? Jeremia ema nosomoni eka indikogi koso?”
18 Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
Baruk nodwoko niya, “En kamano, nowachona wechegi duto to nandikogi, kendo ne andiko gi wino e kitabu.”
19 Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
Eka jotelogo nonyiso Baruk, “In kaachiel gi Jeremia, dhiuru kendo upondi. Kik uwe ngʼato ngʼe kuma untie.”
20 Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
Bangʼ kane giseketo kitabu ei od Elishama jagoro, negidhi ir ruoth e laru kendo giwachone gimoro amora.
21 Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
Ruoth nooro Jehudi mondo okel kitabuno, kendo Jehudi nokele koa kode ei od Elishama jagoro kendo nosomene ruoth kod jotelo duto kochungʼ e bathe.
22 A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
Ne en dwe mar ochiko kendo ruoth nobet ei ot mar oyo mach e kinde mar chwiri.
23 Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
Ka Jehudi nosesomo laini adek kata angʼwen mar kitabuno, ruoth nongʼadogi gi pala mabith kendo owitogi e kar hoyo mach, nyaka kitabuno duto nowangʼ e mach.
24 Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
Ruoth gi jogo duto mane en godo mane owinjo wechegi ne ok obedo gi luoro moro, kata lepgi ne ok giyiecho.
25 Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
Kata obedo ni Elnathan, Delaya kod Gemaria nokwero ruoth mondo kik wangʼ kitabuno, to ne ok onyal winjogi.
26 A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
Makmana, ruoth nomiyo Jeramel, ma wuod ruoth, Seraya wuod Azriel gi Shelemia wuod Abdil chik, mondo omak Baruk jandiko kod Jeremia janabi. To Jehova Nyasaye nosepandogi.
27 Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Bangʼ ka ruoth nosewangʼo kitabu mane otingʼo gik mane Baruk ondiko ka Jeremia somone, wach Jehova Nyasaye nobiro ne Jeremia:
28 “Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
“Kaw kitabu machielo kendo indikie weche duto mane ni e kitabu mokwongo-cha, mane Jehoyakim ruodh Juda owangʼo.
29 Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
Bende nyis Jehoyakim ruodh Juda ni, ‘Ma e gima Jehova Nyasaye wacho: Ne iwangʼo kitabucha kendo iwacho niya, “Angʼo momiyo ne indiko kuome ni ruodh Babulon enobi kendo keth pinyni kendo ogol ji kaachiel gi le kuome?”
30 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
Emomiyo, ma e gima Jehova Nyasaye wacho kuom Jehoyakim ruodh Juda: Ok nobed gi ngʼama bedo e kom duongʼ Daudi; ringre nowit oko kendo nomo oko ne liet mar odiechiengʼ kendo ne thoo mar otieno.
31 Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
Anakume gi nyithinde kod jogo marite nikech timbegi maricho; anakel kuomgi kod jogo modak Jerusalem gi jo-Juda kit masira moro amora mane asechanonegi, nikech gitamore winja.’”
32 Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.
Omiyo Jeremia nokawo kitabu machielo kendo omiye Baruk wuod Neria jandik muma, kendo kaka Jeremia ne ohulo, Baruk nondiko e kitabuno weche duto mar kitabu mane Jehoyakim ruodh Juda nosewangʼo e mach kendo weche mangʼeny machalre nomed kuomgi.