< Irmiya 35 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji a lokacin mulkin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
Слово бывшее ко Иеремии от Господа, во дни Иоакима сына Иосиина, царя Иудина, глаголя:
2 “Ka tafi wurin iyalin Rekabawa ka gayyace su su zo a ɗaya daga cikin ɗakunan da suke gefe a gidan Ubangiji ka kuma ba su ruwan inabi su sha.”
иди в дом Рихавль и призови я и веди я в дом Господень, во един от дворов, и напоиши я вином.
3 Sai na tafi don in kawo Ya’azaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da’yan’uwansa da kuma dukan’ya’yansa maza, dukan iyalin Rekabawa.
И изведох Иезонию сына Иеремиина, сына Хавасиина, и братию его, и сыны его, и весь дом Рихавль,
4 Na kawo su cikin gidan Ubangiji, a cikin ɗakin’ya’yan Hanan ɗan Igdaliya maza mutumin Allah. Ɗakin ne kusa da ɗakin fadawa, wanda yake bisa na Ma’asehiya ɗan Shallum mai tsaron ƙofa.
и введох я в дом Господень, во хранилище имения сынов Анании, сына Годолиина, человека Божия, иже есть близ дому князей, выше дому Маасеова, сына Селомля, стрегущаго двор.
5 Sai na ajiye ƙwarya cike da ruwan inabi da waɗansu kwaf a gaban iyalin Rekabawan na kuma ce musu, “Ku sha ruwan inabin.”
И поставих пред ними корчаг вина и чашы, и рекох: пийте вино.
6 Amma sai suka amsa suka ce, “Ba ma shan ruwan inabi, domin kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko zuriyarku kada ku sha ruwan inabi.
И рекоша: не пием вина, яко Ионадав сын Рихавль, отец наш, заповеда нам, глаголя: не пийте вина вы и сынове ваши до века:
7 Haka kuma ba za ku gina gidaje, ku dasa iri ko ku nome gonakin inabi ba; kada ku kasance da wani daga cikin waɗannan abubuwa, amma dole kullum ku zauna a tentuna. Ta haka za ku yi dogon rai a cikin ƙasar baƙuncinku.’
и храмин да не соградите, и семене не сейте, и виноград да не будет вам, но в кушах да живете вся дни живота вашего, да поживете дни многи на земли, на нейже обитаете вы.
8 Mun yi biyayya da kome da kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu. Mu ko matanmu ko’ya’yanmu maza da mata ba mu taɓa shan ruwan inabi ba
И послушахом словесе Ионадава отца нашего, еже не пити вина вся дни живота нашего, мы и жены нашя, и сынове наши и дщери нашя,
9 ba mu kuma gina gidaje mu zauna a ciki ba ko mu yi gonakin inabi, gonaki ko hatsi ba.
и еже не сограждати храмин жити тамо: и винограда и нивы и семене не бысть нам.
10 Mun yi rayuwarmu a cikin tentuna mun kuma yi biyayya ƙwarai da kowane abin da kakanmu Yehonadab ya umarce mu.
И жихом в кущах, и послушахом и сотворихом по всем, елика заповеда нам Ионадав отец наш.
11 Amma da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasan nan hari, sai muka ce, ‘Ku zo, dole mu tafi Urushalima don mu tsira daga Babiloniyawa da kuma sojojin Arameyawa.’ Saboda haka ne muke a Urushalima.”
И бысть, егда прииде Навуходоносор царь Вавилонский на землю нашу, и рекохом: вшедше да внидем во Иерусалим от лица Халдейска и от лица силы Ассирийския: и вселихомся ту.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
И бысть слово Господне ко Иеремии глаголя:
13 “Ga abin da Ubangiji, Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuda da kuma mutanen Urushalima cewa, ‘Ba za ku koyi darasi ku kuma yi biyayya da maganata ba?’ In ji Ubangiji.
тако глаголет Господь Сил, Бог Израилев: иди и рцы человеку Иудину и живущым во Иерусалиме: еда не восприимете наказания послушати словес Моих?
14 ‘Yehonadab ɗan Rekab ya umarci’ya’yansa maza kada su sha ruwan inabi sun kuma kiyaye wannan umarni. Har yă zuwa yau ba sa shan ruwan inabi, domin sun yi biyayya da umarnin kakansu. Amma na yi muku magana sau da sau, duk da haka ba ku yi biyayya ba.
Утвердиша слово сынове Ионадава, сына Рихавля, еже заповеда сыном своим, еже не пити вина, и не пиша даже до дне сего, яко послушаша заповеди отца своего: Аз же глаголах к вам заутра, и не послушасте Мене:
15 Sau da sau na aika dukan bayina annabawa gare ku. Suka ce, “Kowannenku ya juyo daga mugayen hanyoyinsa ya sabunta ayyukansa; kada yă bi waɗansu alloli don yă bauta musu. Ta haka za ku zauna a cikin ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.” Amma ba ku saurara ba, ba ku kuwa ji ni ba.
и посылах к вам рабы Моя пророки, утренюя и глаголя: обратитеся кийждо от пути своего злаго, и лучше сотворите дела своя, и не ходите вслед богов инех, еже служити им, и вселитеся на земли, юже дах вам и отцем вашым: и не приклонисте ушес ваших и не послушасте.
16 Zuriyar Yehonadab ɗan Rekab sun yi biyayya da umarnin da kakansu ya ba su, amma waɗannan mutane ba su yi mini biyayya ba.’
И уставиша сынове Ионадавли, сына Рихавля, заповедь отца своего, юже заповеда им: а людие Мои не послушаша Мене.
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa Yahuda da kuma kowane mutumin da yake zama a Urushalima kowace masifar da na ambata a kansu. Na yi musu magana, amma ba su saurara ba; na kira su, amma ba su amsa ba.’”
Сего ради сице рече Господь Сил, Бог Израилев: се, Аз наведу на Иуду и на вся живущыя во Иерусалиме вся злая, яже соглаголах на ня: понеже глаголах к ним, и не послушаша, призывах я, и не отвещаша Ми.
18 Sai Irmiya ya ce wa iyalin Rekabawa, “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kun yi biyayya da umarnin kakanku Yehonadab kuka kuma kiyaye dukan umarnansa kuka yi kome bisa ga tsari.’
Дому же Рихавлю рече Иеремиа: тако рече Господь Бог Вседержитель: понеже послушаша сынове Ионадава, сына Рихавля, заповеди отца своего, творити, елика заповеда им отец их:
19 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Yehonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa mutumin da zai yi mini hidima ba.’”
сего ради сия глаголет Господь Сил, Бог Израилев: не оскудеет муж от сынов Ионадавлих, сына Рихавля, стояй пред лицем Моим, вся дни земли.

< Irmiya 35 >