< Irmiya 35 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji a lokacin mulkin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
KA olelo i hiki mai io Ieremia la, mai o Iehova mai i na la o Iehoiakima ke keiki a Iosia, ke alii o ka Iuda, i mai la,
2 “Ka tafi wurin iyalin Rekabawa ka gayyace su su zo a ɗaya daga cikin ɗakunan da suke gefe a gidan Ubangiji ka kuma ba su ruwan inabi su sha.”
O hele oe i ka hale o ka Rekaba, a e olelo aku ia lakou, a e lawe mai ia lakou i ka hale o Iehova, a iloko o kekahi keena, a e hoohainu ia lakou i ka waina.
3 Sai na tafi don in kawo Ya’azaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da’yan’uwansa da kuma dukan’ya’yansa maza, dukan iyalin Rekabawa.
Alaila, kii aku la au ia Iaazania i ke keiki a Ieremia, ke keiki a Habazinia, a me kona poe hoahanau, a me kana mau keikikane a pau, a me ko ka hale a pau o ka Rekaba;
4 Na kawo su cikin gidan Ubangiji, a cikin ɗakin’ya’yan Hanan ɗan Igdaliya maza mutumin Allah. Ɗakin ne kusa da ɗakin fadawa, wanda yake bisa na Ma’asehiya ɗan Shallum mai tsaron ƙofa.
A lawe ae la au ia lakou iloko o ka hale o Iehova, a iloko o ke keena o na keiki a Hanana, ke keiki a Igedalia, he kanaka no ke Akua, aia kokoke i ke keena o na'lii, maluna hoi o ke keena o Maaseia ke keiki a Saluma, ke kiaipuka.
5 Sai na ajiye ƙwarya cike da ruwan inabi da waɗansu kwaf a gaban iyalin Rekabawan na kuma ce musu, “Ku sha ruwan inabin.”
A imua o na kanaka o ka hale o ka Rekaba, kau aku la au i mau ipu i piha i ka waina, a me na kiaha, a i aku la au, E inu oukou i ka waina.
6 Amma sai suka amsa suka ce, “Ba ma shan ruwan inabi, domin kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko zuriyarku kada ku sha ruwan inabi.
Alaila, olelo mai la lakou, Aole makou e inu i ka waina; no ka mea, kauoha mai la o Ionadaba ke keiki a Rekaba ko makou kupuna ia makou, i mai la, Mai inu oukou i ka waina, o oukou, a me ka oukou poe keiki, a i ka manawa pau ole.
7 Haka kuma ba za ku gina gidaje, ku dasa iri ko ku nome gonakin inabi ba; kada ku kasance da wani daga cikin waɗannan abubuwa, amma dole kullum ku zauna a tentuna. Ta haka za ku yi dogon rai a cikin ƙasar baƙuncinku.’
Mai kukulu hale hoi oukou, mai lulu hua, mai kanu pawaina, aole na oukou ia; aka, i ko oukou mau la a pau, e noho oukou ma na halelewa, i nui na la o ko oukou ola ana ma ka aina a oukou i noho malihini ai.
8 Mun yi biyayya da kome da kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu. Mu ko matanmu ko’ya’yanmu maza da mata ba mu taɓa shan ruwan inabi ba
Pela makou i hoolohe ai i ka leo o Ionadaba, ke keiki a Rekaba, ko makou kupunakane, ma na mea a pau ana i kauoha mai ai ia makou, e inu ole i ka waina i ko makou mau la a pau, o makou a me ka makou poe wahine, a me ka makou poe keikikane a me ka makou poe kaikamahine.
9 ba mu kuma gina gidaje mu zauna a ciki ba ko mu yi gonakin inabi, gonaki ko hatsi ba.
Aole hoi e kukulu hale no makou e noho ai iloko; aole hoi o makou pawaiua, aole mahinaai, aole hua.
10 Mun yi rayuwarmu a cikin tentuna mun kuma yi biyayya ƙwarai da kowane abin da kakanmu Yehonadab ya umarce mu.
Aka, ua noho makou ma na halelewa, a ua hoolohe, a ua hana e like me na mea a pau a Ionadaba, ko makou kupuna i Kauoha mai ai ia makou.
11 Amma da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasan nan hari, sai muka ce, ‘Ku zo, dole mu tafi Urushalima don mu tsira daga Babiloniyawa da kuma sojojin Arameyawa.’ Saboda haka ne muke a Urushalima.”
A i ka manawa i pii mai ai i kela aina o Nebukaneza ke alii o Babulona, alaila, i iho la makou, Ea, o haele kakou i Ierusalema no ka makau i ka poe kaua o ko Kaledea, a no ka makau i ka poe kaua o ko Suria; nolaila makou e noho nei i Ierusalema.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Alaila, hiki mai la ka olelo a Iehova ia Ieremia, i mai la,
13 “Ga abin da Ubangiji, Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuda da kuma mutanen Urushalima cewa, ‘Ba za ku koyi darasi ku kuma yi biyayya da maganata ba?’ In ji Ubangiji.
Ke olelo mai nei o Iehova o na kaua, ke Akua o ka Iseraela penei; O hele e hai aku i na kanaka, i ka Iuda, a me ka poe noho ma Ierusalema, Aole anei oukou e ae i ke ao ana, aole anei oukou e hoolohe i ka'u mau olelo? wahi a Iehova.
14 ‘Yehonadab ɗan Rekab ya umarci’ya’yansa maza kada su sha ruwan inabi sun kuma kiyaye wannan umarni. Har yă zuwa yau ba sa shan ruwan inabi, domin sun yi biyayya da umarnin kakansu. Amma na yi muku magana sau da sau, duk da haka ba ku yi biyayya ba.
O na olelo a Ionadaba, ke keiki a Rekaba ana i kauoha iho ai i kana poe keiki, aole e inu i ka waina, ua malamaia. No ka mea, a hiki mai i keia la, ua inu ole lakou, a ua malama hoi i ke kauoha a ka makua. Aka, ua olelo aku no wau ia oukou, e ala ana i ka wanaao e olelo, aole nae oukou i hoolohe mai ia'u.
15 Sau da sau na aika dukan bayina annabawa gare ku. Suka ce, “Kowannenku ya juyo daga mugayen hanyoyinsa ya sabunta ayyukansa; kada yă bi waɗansu alloli don yă bauta musu. Ta haka za ku zauna a cikin ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.” Amma ba ku saurara ba, ba ku kuwa ji ni ba.
Ua hoouna aku no hoi au io oukou la, i ka'u poe kauwa a pau, i na kaula, e ala ana i ka wanaao e hoouna, me ka olelo aku, E hoi mai kela mea keia mea o oukou, mai kona aoao hewa mai, a e hooponopono i ka oukou hana ana; a mai hele mahope o na akua e, e malama ia lakou, a e noho no oukou ma ka aina a'u i haawi aku ai ia oukou, a i ko oukou poe makua; aole nae oukou i haliu mai i ko oukou pepeiao, aole i hoolohe mai ia'u.
16 Zuriyar Yehonadab ɗan Rekab sun yi biyayya da umarnin da kakansu ya ba su, amma waɗannan mutane ba su yi mini biyayya ba.’
No ka mea, ua malama na keiki a Ionadaba, ke keiki a Rekaba i ke kauoha o ko lakou makua, ana i kauoha ai ia lakou; a ua hoolohe ole keia poe kanaka ia'u:
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa Yahuda da kuma kowane mutumin da yake zama a Urushalima kowace masifar da na ambata a kansu. Na yi musu magana, amma ba su saurara ba; na kira su, amma ba su amsa ba.’”
Nolaila, ke olelo mai nei o Iehova, ke Akua o na kaua, ke Akua o ka Iseraela; Aia hoi, E lawe mai no wau maluna o ka Iuda, a maluna o ka poe a pau e noho la ma Ierusalema i ka hewa a pau a'u i olelo ai ia lakou: no ka mea, ua olelo no wau ia lakou, aole lakou i lohe mai; ua hea aku au ia lakou, aole lakou i o mai.
18 Sai Irmiya ya ce wa iyalin Rekabawa, “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kun yi biyayya da umarnin kakanku Yehonadab kuka kuma kiyaye dukan umarnansa kuka yi kome bisa ga tsari.’
Olelo ae la o Ieremia i ko ka hale o ka Rekaba, Ke olelo mai nei o Iehova o na kaua, ke Akua o ka Iseraela, penei; No ka mea, ua hoolohe oukou i ke kauoha a Ionadaba, ko oukou kupunakane, a malama hoi i kona mau kanawai, a ua hana e like me ua mea a pau aua i kauoha mai ai ia oukou;
19 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Yehonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa mutumin da zai yi mini hidima ba.’”
Nolaila, ke olelo mai nei o Iehova o na kaua, ke Akua o ka Iseraela, Aole e nele o Ionadaba, ke keiki a Rekaba, i ke kanaka e ku imua o'u, a hiki i ka manawa pau ole.

< Irmiya 35 >