< Irmiya 35 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji a lokacin mulkin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
La parole qui fut adressée par l'Éternel à Jérémie, aux jours de Jéhojakim, fils de Josias, roi de Juda, en ces termes:
2 “Ka tafi wurin iyalin Rekabawa ka gayyace su su zo a ɗaya daga cikin ɗakunan da suke gefe a gidan Ubangiji ka kuma ba su ruwan inabi su sha.”
Va à la maison des Récabites, et leur parle, et fais-les venir à la maison de l'Éternel, dans une des chambres, et offre-leur du vin à boire.
3 Sai na tafi don in kawo Ya’azaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da’yan’uwansa da kuma dukan’ya’yansa maza, dukan iyalin Rekabawa.
Je pris donc Jaazania, fils de Jérémie, fils de Habatsinia, et ses frères, et tous ses fils, et toute la maison des Récabites;
4 Na kawo su cikin gidan Ubangiji, a cikin ɗakin’ya’yan Hanan ɗan Igdaliya maza mutumin Allah. Ɗakin ne kusa da ɗakin fadawa, wanda yake bisa na Ma’asehiya ɗan Shallum mai tsaron ƙofa.
Et je les amenai à la maison de l'Éternel, dans la chambre des fils de Hanan, fils de Jigdalia, homme de Dieu, laquelle était auprès de la chambre des chefs, au-dessus de la chambre de Maaséja, fils de Shallum, garde du seuil.
5 Sai na ajiye ƙwarya cike da ruwan inabi da waɗansu kwaf a gaban iyalin Rekabawan na kuma ce musu, “Ku sha ruwan inabin.”
Et je mis devant les enfants de la maison des Récabites des vases pleins de vin et des coupes, et je leur dis: Buvez du vin!
6 Amma sai suka amsa suka ce, “Ba ma shan ruwan inabi, domin kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko zuriyarku kada ku sha ruwan inabi.
Mais ils répondirent: Nous ne boirons point de vin; car Jonadab, fils de Récab, notre père, nous a donné un ordre en disant: Vous ne boirez point de vin, ni vous ni vos enfants, à jamais;
7 Haka kuma ba za ku gina gidaje, ku dasa iri ko ku nome gonakin inabi ba; kada ku kasance da wani daga cikin waɗannan abubuwa, amma dole kullum ku zauna a tentuna. Ta haka za ku yi dogon rai a cikin ƙasar baƙuncinku.’
Vous ne bâtirez point de maisons; vous ne sèmerez pas de semence; vous ne planterez pas de vigne, et vous n'en posséderez point; mais vous habiterez sous des tentes, tous les jours de votre vie, afin que vous viviez longtemps sur la terre où vous êtes étrangers.
8 Mun yi biyayya da kome da kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu. Mu ko matanmu ko’ya’yanmu maza da mata ba mu taɓa shan ruwan inabi ba
Et nous avons obéi à la voix de Jonadab, fils de Récab, notre père, en tout ce qu'il nous a prescrit; de sorte que nous ne buvons pas de vin pendant toute notre vie, ni nous, ni nos femmes, ni nos fils, ni nos filles;
9 ba mu kuma gina gidaje mu zauna a ciki ba ko mu yi gonakin inabi, gonaki ko hatsi ba.
Nous n'avons point bâti de maisons pour notre demeure, et nous ne possédons ni vignes, ni champs, ni semailles,
10 Mun yi rayuwarmu a cikin tentuna mun kuma yi biyayya ƙwarai da kowane abin da kakanmu Yehonadab ya umarce mu.
Mais nous avons habité sous des tentes, et nous avons obéi, et fait tout ce que nous a prescrit Jonadab, notre père.
11 Amma da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasan nan hari, sai muka ce, ‘Ku zo, dole mu tafi Urushalima don mu tsira daga Babiloniyawa da kuma sojojin Arameyawa.’ Saboda haka ne muke a Urushalima.”
Or, quand Nébucadnetsar, roi de Babylone, est monté contre ce pays, nous avons dit: Venez, retirons-nous à Jérusalem, loin de l'armée des Caldéens et de l'armée de Syrie. C'est ainsi que nous habitons à Jérusalem.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Alors la parole de l'Éternel fut adressée à Jérémie, en ces mots:
13 “Ga abin da Ubangiji, Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuda da kuma mutanen Urushalima cewa, ‘Ba za ku koyi darasi ku kuma yi biyayya da maganata ba?’ In ji Ubangiji.
Ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël: Va, et dis aux hommes de Juda, et aux habitants de Jérusalem: Ne recevrez-vous pas instruction, pour obéir à mes paroles? dit l'Éternel.
14 ‘Yehonadab ɗan Rekab ya umarci’ya’yansa maza kada su sha ruwan inabi sun kuma kiyaye wannan umarni. Har yă zuwa yau ba sa shan ruwan inabi, domin sun yi biyayya da umarnin kakansu. Amma na yi muku magana sau da sau, duk da haka ba ku yi biyayya ba.
On a observé la parole de Jonadab, fils de Récab, qui a ordonné à ses fils de ne pas boire de vin; ils n'en ont point bu jusqu'à ce jour, car ils ont obéi à l'ordre de leur père. Mais moi, je vous ai parlé, parlé dès le matin, et vous ne m'avez pas obéi.
15 Sau da sau na aika dukan bayina annabawa gare ku. Suka ce, “Kowannenku ya juyo daga mugayen hanyoyinsa ya sabunta ayyukansa; kada yă bi waɗansu alloli don yă bauta musu. Ta haka za ku zauna a cikin ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.” Amma ba ku saurara ba, ba ku kuwa ji ni ba.
Je vous ai envoyé tous mes serviteurs, les prophètes; je les ai envoyés dès le matin pour vous dire: Détournez-vous chacun de votre mauvaise voie; amendez vos actions, et n'allez pas après d'autres dieux pour les servir; et vous demeurerez dans le pays que j'ai donné à vous et à vos pères. Mais vous n'avez pas prêté l'oreille, et vous ne m'avez pas écouté.
16 Zuriyar Yehonadab ɗan Rekab sun yi biyayya da umarnin da kakansu ya ba su, amma waɗannan mutane ba su yi mini biyayya ba.’
Oui, les fils de Jonadab, fils de Récab, ont observé l'ordre que leur père leur avait donné, et ce peuple ne m'a point écouté!
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa Yahuda da kuma kowane mutumin da yake zama a Urushalima kowace masifar da na ambata a kansu. Na yi musu magana, amma ba su saurara ba; na kira su, amma ba su amsa ba.’”
C'est pourquoi l'Éternel, le Dieu des armées, le Dieu d'Israël, dit ainsi: Voici, je vais faire venir sur Juda et sur tous les habitants de Jérusalem tout le mal que j'ai prononcé contre eux, parce que je leur ai parlé, et qu'ils n'ont pas écouté; que je les ai appelés, et qu'ils n'ont pas répondu.
18 Sai Irmiya ya ce wa iyalin Rekabawa, “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kun yi biyayya da umarnin kakanku Yehonadab kuka kuma kiyaye dukan umarnansa kuka yi kome bisa ga tsari.’
Puis Jérémie dit à la maison des Récabites: Ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël: Parce que vous avez obéi à l'ordre de Jonadab, votre père, et que vous avez gardé tous ses commandements et fait selon tout ce qu'il vous a prescrit,
19 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Yehonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa mutumin da zai yi mini hidima ba.’”
A cause de cela, ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël: Jonadab, fils de Récab, ne manquera jamais de descendants qui se tiennent devant ma face.

< Irmiya 35 >