< Irmiya 35 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji a lokacin mulkin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
C'est ici la parole qui fut [adressée] par l'Eternel à Jérémie, aux jours de Jéhojakim, fils de Josias Roi de Juda, en disant:
2 “Ka tafi wurin iyalin Rekabawa ka gayyace su su zo a ɗaya daga cikin ɗakunan da suke gefe a gidan Ubangiji ka kuma ba su ruwan inabi su sha.”
Va à la maison des Récabites, et leur parle, et les fais venir en la maison de l'Eternel, dans l'une des chambres, et présente-leur du vin à boire.
3 Sai na tafi don in kawo Ya’azaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da’yan’uwansa da kuma dukan’ya’yansa maza, dukan iyalin Rekabawa.
Je pris donc Jaazanja fils de Jérémie, fils de Habatsinja, et ses frères, et tous ses fils, et toute la maison des Récabites;
4 Na kawo su cikin gidan Ubangiji, a cikin ɗakin’ya’yan Hanan ɗan Igdaliya maza mutumin Allah. Ɗakin ne kusa da ɗakin fadawa, wanda yake bisa na Ma’asehiya ɗan Shallum mai tsaron ƙofa.
Et je les fis venir dans la maison de l'Eternel, en la chambre des fils de Hanan, fils de Jigdalia, homme de Dieu, laquelle était près de la chambre des principaux; qui était sur la chambre de Mahaséja, fils de Sallum, garde des vaisseaux.
5 Sai na ajiye ƙwarya cike da ruwan inabi da waɗansu kwaf a gaban iyalin Rekabawan na kuma ce musu, “Ku sha ruwan inabin.”
Et je mis devant les enfants de la maison des Récabites, des gobelets pleins de vin, et des tasses, et je leur dis: buvez du vin.
6 Amma sai suka amsa suka ce, “Ba ma shan ruwan inabi, domin kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko zuriyarku kada ku sha ruwan inabi.
Et ils répondirent: nous ne boirons point de vin; car Jéhonadab, fils de Récab notre père nous a donné un commandement, en disant: vous ne boirez point de vin, ni vous, ni vos enfants, à jamais;
7 Haka kuma ba za ku gina gidaje, ku dasa iri ko ku nome gonakin inabi ba; kada ku kasance da wani daga cikin waɗannan abubuwa, amma dole kullum ku zauna a tentuna. Ta haka za ku yi dogon rai a cikin ƙasar baƙuncinku.’
Vous ne bâtirez aucune maison, vous ne sèmerez aucune semence, vous ne planterez aucune vigne, et vous n'en aurez point; mais vous habiterez en des tentes tous les jours de votre vie, afin que vous viviez longtemps sur la terre dans laquelle vous séjournez comme étrangers.
8 Mun yi biyayya da kome da kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu. Mu ko matanmu ko’ya’yanmu maza da mata ba mu taɓa shan ruwan inabi ba
Nous avons donc obéi à la voix de Jéhonadab, fils de Récab notre père, dans toutes les choses qu'il nous a commandées, de sorte que nous n'avons point bu de vin tous les jours de notre vie, ni nous, [ni] nos femmes, ni nos fils, ni nos filles.
9 ba mu kuma gina gidaje mu zauna a ciki ba ko mu yi gonakin inabi, gonaki ko hatsi ba.
Nous n'avons bâti aucune maison pour notre demeure, et nous n'avons eu ni vigne, ni champ, ni semence.
10 Mun yi rayuwarmu a cikin tentuna mun kuma yi biyayya ƙwarai da kowane abin da kakanmu Yehonadab ya umarce mu.
Mais nous avons demeuré dans des tentes, et nous avons obéi, et avons fait selon toutes les choses que Jéhonadab notre père nous a commandées.
11 Amma da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasan nan hari, sai muka ce, ‘Ku zo, dole mu tafi Urushalima don mu tsira daga Babiloniyawa da kuma sojojin Arameyawa.’ Saboda haka ne muke a Urushalima.”
Mais il est arrivé que quand Nébucadnetsar Roi de Babylone est monté au pays, nous avons dit: venez, et entrons dans Jérusalem pour fuir de devant l'armée des Caldéens, et de devant l'armée de Syrie; et nous sommes demeurés dans Jérusalem.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Alors la parole de l'Eternel fut [adressée] à Jérémie, en disant:
13 “Ga abin da Ubangiji, Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuda da kuma mutanen Urushalima cewa, ‘Ba za ku koyi darasi ku kuma yi biyayya da maganata ba?’ In ji Ubangiji.
Ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: va, et dis aux hommes de Juda, et aux habitants de Jérusalem: ne recevrez-vous point d'instruction pour obéir à mes paroles? dit l'Eternel.
14 ‘Yehonadab ɗan Rekab ya umarci’ya’yansa maza kada su sha ruwan inabi sun kuma kiyaye wannan umarni. Har yă zuwa yau ba sa shan ruwan inabi, domin sun yi biyayya da umarnin kakansu. Amma na yi muku magana sau da sau, duk da haka ba ku yi biyayya ba.
Toutes les paroles de Jéhonadab, fils de Récab, qu'il a commandées à ses enfants de ne boire point de vin, ont été observées, et ils n'[en] ont point bu jusques à ce jour; mais ils ont obéi au commandement de leur père; mais moi je vous ai parlé, me levant dès le matin, et parlant, et vous ne m'avez point obéi.
15 Sau da sau na aika dukan bayina annabawa gare ku. Suka ce, “Kowannenku ya juyo daga mugayen hanyoyinsa ya sabunta ayyukansa; kada yă bi waɗansu alloli don yă bauta musu. Ta haka za ku zauna a cikin ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.” Amma ba ku saurara ba, ba ku kuwa ji ni ba.
Car je vous ai envoyé tous les Prophètes, mes serviteurs, me levant dès le matin, et les envoyant, pour vous dire: détournez-vous maintenant chacun de son mauvais train, et corrigez vos actions, et ne suivez point d'autres dieux pour les servir, afin que vous demeuriez en la terre que j'ai donnée à vous et à vos pères; mais vous n'avez point incliné vos oreilles, et ne m'avez point écouté.
16 Zuriyar Yehonadab ɗan Rekab sun yi biyayya da umarnin da kakansu ya ba su, amma waɗannan mutane ba su yi mini biyayya ba.’
Parce que les enfants de Jéhonadab fils de Récab ont observé le commandement de leur père, lequel il leur avait fait, et que ce peuple ne m'a point écouté;
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa Yahuda da kuma kowane mutumin da yake zama a Urushalima kowace masifar da na ambata a kansu. Na yi musu magana, amma ba su saurara ba; na kira su, amma ba su amsa ba.’”
A cause de cela l'Eternel le Dieu des armées, le Dieu d'Israël, dit ainsi: voici, je m'en vais faire venir sur Juda et sur tous les habitants de Jérusalem tout le mal que j'ai prononcé contre eux; parce que je leur ai parlé, et ils n'ont point écouté; et que je les ai appelés, et ils n'ont point répondu.
18 Sai Irmiya ya ce wa iyalin Rekabawa, “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kun yi biyayya da umarnin kakanku Yehonadab kuka kuma kiyaye dukan umarnansa kuka yi kome bisa ga tsari.’
Et Jérémie dit à la maison des Récabites: ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: parce que vous avez obéi au commandement de Jéhonadab votre père, et que vous avez gardé tous ses commandements, et avez fait selon tout ce qu'il vous a commandé;
19 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Yehonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa mutumin da zai yi mini hidima ba.’”
C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: il n'arrivera jamais qu'il n'y ait quelqu'un appartenant à Jéhonadab fils de Récab, qui assiste devant moi tous les jours.

< Irmiya 35 >