< Irmiya 35 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji a lokacin mulkin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
The word that came to Jeremiah from the Lord, [in] the days of Jehoyakim the son of Josiah the king of Judah, saying,
2 “Ka tafi wurin iyalin Rekabawa ka gayyace su su zo a ɗaya daga cikin ɗakunan da suke gefe a gidan Ubangiji ka kuma ba su ruwan inabi su sha.”
Go unto the house of the Rechabites, and speak with them, and bring them into the house of the Lord, into one of the chambers, and offer them wine to drink.
3 Sai na tafi don in kawo Ya’azaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da’yan’uwansa da kuma dukan’ya’yansa maza, dukan iyalin Rekabawa.
Then I took Yaazanyah the son of Jeremiah, the son of Chabazzinyah, and his brethren, and all his sons, and the whole house of the Rechabites;
4 Na kawo su cikin gidan Ubangiji, a cikin ɗakin’ya’yan Hanan ɗan Igdaliya maza mutumin Allah. Ɗakin ne kusa da ɗakin fadawa, wanda yake bisa na Ma’asehiya ɗan Shallum mai tsaron ƙofa.
And I brought them into the house of the Lord, into the chamber of the sons of Chanan, the son of Yigdalyahu, the man of God, which was alongside of the chamber of the princes, which was above the chamber of Ma'aseyahu the son of Shallum, the keeper of the door:
5 Sai na ajiye ƙwarya cike da ruwan inabi da waɗansu kwaf a gaban iyalin Rekabawan na kuma ce musu, “Ku sha ruwan inabin.”
And I set before the sons of the house of the Rechabites goblets full of wine, and cups; and I said unto them, Drink wine.
6 Amma sai suka amsa suka ce, “Ba ma shan ruwan inabi, domin kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko zuriyarku kada ku sha ruwan inabi.
But they said, We will not drink wine; for Jonadab the son of Rechab our father hath laid a charge on us, saying, Ye shall not drink wine, neither ye, nor your sons for ever;
7 Haka kuma ba za ku gina gidaje, ku dasa iri ko ku nome gonakin inabi ba; kada ku kasance da wani daga cikin waɗannan abubuwa, amma dole kullum ku zauna a tentuna. Ta haka za ku yi dogon rai a cikin ƙasar baƙuncinku.’
Nor shall ye build any house, nor sow seed, nor plant a vineyard, nor have [any such]; but in tents shall ye dwell all your days, in order that ye may live many days on the face of the land where ye may sojourn.
8 Mun yi biyayya da kome da kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu. Mu ko matanmu ko’ya’yanmu maza da mata ba mu taɓa shan ruwan inabi ba
And we have hearkened unto the voice of Jehonadab the son of Rechab our father in all that he hath charged us, not to drink any wine all our days, we, our wives, our sons, and our daughters;
9 ba mu kuma gina gidaje mu zauna a ciki ba ko mu yi gonakin inabi, gonaki ko hatsi ba.
And not to build houses for our dwelling: and we never had any vineyard, or field, or seed;
10 Mun yi rayuwarmu a cikin tentuna mun kuma yi biyayya ƙwarai da kowane abin da kakanmu Yehonadab ya umarce mu.
But we have dwelt in tents, and have obeyed, and done in accordance with all that Jonadab our father commanded us.
11 Amma da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasan nan hari, sai muka ce, ‘Ku zo, dole mu tafi Urushalima don mu tsira daga Babiloniyawa da kuma sojojin Arameyawa.’ Saboda haka ne muke a Urushalima.”
But it came to pass, when Nebuchadrezzar the king of Babylon came up into the land, that we said, Come, and let us go into Jerusalem because of the army of the Chaldeans, and because of the army of the Syrians; and so we dwell at Jerusalem.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Then came the word of the Lord unto Jeremiah, saying,
13 “Ga abin da Ubangiji, Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuda da kuma mutanen Urushalima cewa, ‘Ba za ku koyi darasi ku kuma yi biyayya da maganata ba?’ In ji Ubangiji.
Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Go and say to the men of Judah and to the inhabitants of Jerusalem, Will ye not receive instruction to hearken to my words? saith the Lord.
14 ‘Yehonadab ɗan Rekab ya umarci’ya’yansa maza kada su sha ruwan inabi sun kuma kiyaye wannan umarni. Har yă zuwa yau ba sa shan ruwan inabi, domin sun yi biyayya da umarnin kakansu. Amma na yi muku magana sau da sau, duk da haka ba ku yi biyayya ba.
Fulfilled are the words of Jehonadab the son of Rechab, that he hath commanded his sons not to drink wine: and they have not drunk any even unto this day; because they have obeyed the commandment of their father; but I, I have spoken unto you, early in the day and speaking; but ye have not hearkened unto me.
15 Sau da sau na aika dukan bayina annabawa gare ku. Suka ce, “Kowannenku ya juyo daga mugayen hanyoyinsa ya sabunta ayyukansa; kada yă bi waɗansu alloli don yă bauta musu. Ta haka za ku zauna a cikin ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.” Amma ba ku saurara ba, ba ku kuwa ji ni ba.
And I have sent unto you all my servants the prophets, making them rise up early and sending them, saying, Do but return every man from his evil way, and amend your deeds, and go not after other gods to serve them: and so shall ye remain in the land which I have given to you and to your fathers; but ye have not inclined your ear, and have not hearkened unto me.
16 Zuriyar Yehonadab ɗan Rekab sun yi biyayya da umarnin da kakansu ya ba su, amma waɗannan mutane ba su yi mini biyayya ba.’
Because the sons of Jehonadab the son of Rechab have fulfilled the commandment of their father, which he hath commanded them; but as this people have not hearkened unto me:
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa Yahuda da kuma kowane mutumin da yake zama a Urushalima kowace masifar da na ambata a kansu. Na yi musu magana, amma ba su saurara ba; na kira su, amma ba su amsa ba.’”
Therefore thus hath said the Lord, the God of hosts, the God of Israel, Behold, I will bring upon Judah and upon all the inhabitants of Jerusalem all the evil that I have spoken concerning them; because I spoke unto them, but they would not hear; and I called unto them, but they would not answer.
18 Sai Irmiya ya ce wa iyalin Rekabawa, “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kun yi biyayya da umarnin kakanku Yehonadab kuka kuma kiyaye dukan umarnansa kuka yi kome bisa ga tsari.’
And unto the house of the Rechabites said Jeremiah, Thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, Whereas ye have hearkened to the charge of Jonadab your father, and have kept all his commandments, and have done in accordance with all that he hath commanded you:
19 Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Yehonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa mutumin da zai yi mini hidima ba.’”
Therefore thus hath said the Lord of hosts, the God of Israel, There shall not be wanting unto Jehonadab the son of Rechab a man to stand before me at all times.

< Irmiya 35 >