< Irmiya 34 >

1 Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
Rijeè koja doðe Jeremiji od Gospoda, kad Navuhodonosor car Vavilonski i sva vojska njegova, i sva carstva zemaljska koja bijahu pod njegovom vlašæu, i svi narodi vojevahu na Jerusalim i na sve gradove njegove, i reèe:
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
Ovako veli Gospod Bog Izrailjev: idi i kaži Sedekiji caru Judinu i reci mu: ovako veli Gospod: evo, ja æu predati taj grad u ruke caru Vavilonskom, i on æe ga spaliti ognjem.
3 Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
A ti neæeš uteæi iz njegove ruke, nego æeš biti uhvaæen i predan u njegove ruke, i oèi æe se tvoje vidjeti s oèima cara Vavilonskoga i njegova æe usta govoriti s tvojim ustima, i otiæi æeš u Vavilon.
4 “‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
Ali èuj rijeè Gospodnju, Sedekija care Judin; ovako veli Gospod za te: neæeš poginuti od maèa.
5 za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
Nego æeš umrijeti na miru, i kao što pališe ocima tvojima, preðašnjim carevima, koji su bili prije tebe, tako æe paliti i tebi, i naricaæe za tobom: jaoh gospodaru! jer ja rekoh ovo, govori Gospod.
6 Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
I kaza Jeremija prorok Sedekiji caru Judinu sve ove rijeèi u Jerusalimu.
7 yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
A vojska cara Vavilonskoga udaraše na Jerusalim i na sve ostale gradove Judine, na Lahis i Aziku, jer ti bjehu ostali tvrdi gradovi izmeðu gradova Judinijeh.
8 Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
Rijeè koja doðe Jeremiji od Gospoda kad car Sedekija uèini zavjet sa svijem narodom koji bješe u Jerusalimu da im proglasi slobodu,
9 Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
Da svaki otpusti slobodna roba svojega i robinju svoju, Jevrejina i Jevrejku, da ni u koga ne bude rob Judejac brat njegov.
10 Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
I poslušaše svi knezovi i sav narod, koji prista na zavjet, da svaki otpusti slobodna roba svojega i robinju svoju, da im ne budu više robovi, poslušaše i otpustiše.
11 Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
A poslije opet staše uzimati robove i robinje, koje bijahu otpustili na volju, i nagoniše ih da im budu robovi i robinje.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
I doðe rijeè Gospodnja Jeremiji od Gospoda govoreæi:
13 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
Ovako veli Gospod Bog Izrailjev: ja uèinih zavjet s ocima vašim kad vas izvedoh iz zemlje Misirske, iz doma ropskoga, govoreæi:
14 ‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
Kad se svršuje sedma godina, otpuštajte svaki brata svojega Jevrejina koji ti se bude prodao i služio ti šest godina, otpusti ga slobodna od sebe. Ali ne poslušaše me oci vaši niti prignuše uha svojega.
15 Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
I vi se bjeste sada obratili i uèinili što je pravo preda mnom proglasivši slobodu svaki bližnjemu svojemu, uèinivši zavjet preda mnom u domu koji se zove mojim imenom.
16 Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
Ali udariste natrag i pogrdiste ime moje uzevši opet svaki roba svojega i robinju svoju, koje bijaste otpustili slobodne na njihovu volju, i natjeraste ih da vam budu robovi i robinje.
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
Zato ovako veli Gospod: vi ne poslušaste mene da proglasite slobodu svaki bratu svojemu i bližnjemu svojemu; evo, ja proglašujem slobodu suprot vama, govori Gospod, maèu, pomoru i gladi, i predaæu vas da se potucate po svijem carstvima zemaljskim.
18 Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
I predaæu ljude koji prestupiše moj zavjet, koji ne izvršiše rijeèi zavjeta koji uèiniše preda mnom, rasjekavši tele na dvoje i prošavši izmeðu polovina,
19 Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
Knezove Judine i knezove Jerusalimske, dvorane i sveštenike i sav narod ove zemlje, koji proðoše izmeðu polovina onoga teleta,
20 zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
Predaæu ih u ruke neprijateljima njihovijem i u ruke onima koji traže dušu njihovu, i mrtva æe tijela njihova biti hrana pticama nebeskim i zvijerima zemaljskim.
21 “Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
I Sedekiju cara Judina i knezove njegove predaæu u ruke neprijateljima njihovijem i u ruke onima koji traže dušu njihovu, u ruke vojsci cara Vavilonskoga, koja se vratila od vas.
22 Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”
Evo, ja æu im zapovjediti, veli Gospod, i dovešæu ih opet na ovaj grad, i biæe ga i uzeæe ga i spaliæe ga ognjem; i gradove Judine obratiæu u pustoš da niko neæe stanovati u njima.

< Irmiya 34 >