< Irmiya 34 >

1 Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
Parole qui fut adressée à Jérémie par le Seigneur, lorsque Nabuchodonosor, roi de Babylone, et toute son armée, et tous les royaumes de la terre qui étaient sous le pouvoir de sa main, et tous les peuples combattaient contre Jérusalem et contre toutes ses villes, disant:
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
Voici ce que dit le Seigneur, Dieu d’Israël: Va, et parle à Sédécias, roi de Juda; et tu lui diras: Voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi, je livrerai cette cité aux mains du roi de Babylone, et il y mettra le feu.
3 Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
Et toi tu n’échapperas pas à sa main, mais tu seras pris très certainement, et tu seras livré à sa main: et tes yeux verront les yeux du roi de Babylone, et sa bouche parlera à ta bouche, et tu entreras à Babylone.
4 “‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
Cependant écoute la parole du Seigneur, Sédécias, roi de Juda; voici ce que te dit le Seigneur: Tu ne mourras point par le glaive.
5 za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
Mais tu mourras en paix; et comme on a brûlé les corps de tes pères, des rois précédents qui ont été avant toi, ainsi on te brûlera; et malheur, ô prince! criera-t-on sur toi; parce que c’est moi qui ai prononcé cette parole, dit le Seigneur.
6 Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
Et Jérémie, le prophète, dit toutes ces paroles à Sédécias, roi de Juda, dans Jérusalem.
7 yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
Et l’armée du roi de Babylone combattait contre Jérusalem, et contre toutes les cités de Juda qui étaient restées, contre Lachis et contre Azécha; car c’étaient les villes fortifiées, qui étaient restées des cités de Juda.
8 Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
Parole qui fut adressée à Jérémie par le Seigneur, après que le roi Sédécias eut fait un pacte avec tout le peuple dans Jérusalem, en publiant
9 Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
Que chacun renvoyât libre son serviteur et chacun sa servante, Hébreu et Hébreue, et qu’ils n’exerçassent nullement leur domination sur eux, c’est-à-dire sur un Juif et leur frère.
10 Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
Ils entendirent donc tous les princes et tout le peuple, qui avaient fait pacte que chacun renverrait libre son serviteur et chacun sa servante, et qu’ils n’exerceraient plus de domination sur eux; ils écoutèrent donc et les renvoyèrent.
11 Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
Mais ils changèrent ensuite, et ils reprirent leurs serviteurs et leurs servantes qu’ils avaient renvoyés libres, et les soumirent à la condition de serviteurs et de servantes.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie, disant:
13 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
Voici ce que dit le Seigneur, Dieu d’Israël: Moi, j’ai fait alliance avec vos pères au jour où je les ai retirés de la terre d’Egypte, de la maison de servitude, disant:
14 ‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
Lorsque sept ans seront accomplis, que chacun renvoie son frère Hébreu, qui lui a été vendu; il te servira six ans, puis tu le renverras d’auprès de toi libre; et vos pères ne m’ont point écouté et ils n’ont pas incliné leur oreille.
15 Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
Et vous, vous êtes tournés vers moi aujourd’hui; vous avez fait ce qui était juste à mes yeux, en publiant la liberté chacun pour son ami; et vous avez fait ce pacte en ma présence, dans la maison dans laquelle mon nom a été invoqué sur elle.
16 Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
Et vous êtes revenus sur ce que vous aviez fait, et vous avez profané mon nom; et vous avez repris chacun votre esclave et chacun votre servante, que vous aviez renvoyés afin qu’ils fussent libres, et en leur propre pouvoir, et vous les avez réduits à vous être serviteurs et servantes.
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
À cause de cela voici ce que dit le Seigneur: Vous, vous ne m’avez pas écouté pour annoncer la liberté chacun à votre frère et chacun à votre ami; voici que moi, dit le Seigneur, je vous annonce la liberté d’être abandonnés au glaive, à la peste et à la famine; je vous livrerai à la vexation dans tous les royaumes de la terre.
18 Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
Et je traiterai les hommes qui violent mon alliance, et qui n’ont pas observé les paroles du pacte auxquelles ils ont consenti en ma présence, comme le veau qu’ils ont coupé en deux, et entre les parties duquel ils ont passé;
19 Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
Ces hommes sont les princes de Juda, les princes de Jérusalem, les eunuques et les prêtres, et tout le peuple de cette terre, qui ont passé entre les parties du veau;
20 zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
Je les livrerai donc aux mains de leurs ennemis, aux mains de ceux qui cherchent leur âme; et leurs corps morts seront en pâture aux volatiles du ciel et aux bêtes de la terre.
21 “Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
Et Sédécias, roi de Juda, et ses princes, je les livrerai aux mains de leurs ennemis, et aux mains de ceux qui cherchent leurs âmes, et aux mains des armées du roi de Babylone, lesquelles se sont retirées de vous.
22 Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”
Voilà que moi j’ordonne, dit le Seigneur, je les ramènerai dans cette cité, et ils combattront contre elle, et ils la prendront, et ils y mettront le feu; et les cités de Juda, j’en ferai une solitude pour qu’il n’y ait point d’habitant.

< Irmiya 34 >