< Irmiya 34 >
1 Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
The word which came unto Jeremiah from Yahweh, —when Nebuchadnezzar king of Babylon and all his force and all the kingdoms of the earth the dominion of his hand, and all the peoples were fighting against Jerusalem and against all her cities, saying:
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
Thus, saith Yahweh God of Israel, Go and speak unto Zedekiah king of Judah, —and say unto him—Thus, saith Yahweh, Behold me! giving this city into the hand of the king of Babylon, and he will burn it with fire;
3 Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
And, thou, shalt not escape out of his hand, For thou shalt be, taken, And into his hand, shalt thou be delivered, —And, thine own eyes, into the eyes of the king of Babylon, shall look, And his mouth, with thy mouth, shall speak And Babylon, shalt thou enter.
4 “‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
Nevertheless, hear the word of Yahweh, O Zedekiah, king of Judah, —Thus, saith Yahweh Concerning thee, Thou shalt not die, by the sword;
5 za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
In peace, shalt thou die, And with the burnings made for thy fathers the former kings who were before thee, so, shall they make a burning unto thee, And, with an, Alas lord! shall they lament thee, —Because of the word, I, have spoken, Declareth Yahweh.
6 Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
Then spake Jeremiah the prophet, unto Zedekiah king of Judah all these words in Jerusalem;
7 yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
when, the force of the king of Babylon, was fighting against Jerusalem, and against all the cities of Judah that were left, —against Lachish and against Azekah, for they, remained among the cities of Judah as fortified cities.
8 Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
The word which came unto Jeremiah, from Yahweh, —after that King Zedekiah had solemnised a covenant with all the people who were in Jerusalem, proclaiming unto them liberty:
9 Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
that every man should let his servant and every man his handmaid, being a Hebrew or a Hebrewess, go free, —so that no man should use them as slaves, to wit a Jew his brother;
10 Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
so then they hearkened—even all the princes and all the people who had entered into the covenant that every man should let his servant and every man his handmaid, go free, so as not to use them as slaves, any longer, —yea they hearkened, and let them go,
11 Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
howbeit they turned after that, and brought back the servants and the handmaids whom they had let go, free, and brought them into subjection as servants and as handmaids,
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
So then the word of Yahweh came unto Jeremiah from Yahweh, saying:
13 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
Thus, saith Yahweh God of Israel, —I myself, solemnised a covenant with your fathers, in the day when I brought them forth out of the land of Egypt, out of the house of slaves saying:
14 ‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
At the end of seven years, shall ye let go every man his brother, being a Hebrew, who shall sell himself unto thee and serve thee, six years, then shalt thou let him go, free, from thee, Howbeit your fathers hearkened not unto me neither inclined their ear.
15 Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
And, though, ye, just now turned and did that which was right in mine eyes, by proclaiming liberty, every man to his neighbour, —and solemnised a covenant before me, in the house on which my Name hath been called,
16 Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
yet have ye turned and profaned my Name, and brought back, every man his servant and every man his hand-maid, whom ye had let go, free, at their own desire, —and have brought them into subjection, to become your servants and handmaids.
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
Therefore—Thus, saith Yahweh, Ye, have not hearkened unto me, in proclaiming liberty, every man to his brother and every man to his neighbour: Behold me! proclaiming, to you, a liberty: Declareth Yahweh unto the sword, unto the pestilence, and unto the famine, so will I make you a terror to all the kingdoms of the earth;
18 Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
and will give the men who are transgressing my covenant, in that they have not confirmed the words of the covenant, which they solemnised, before me, when they cut the calf, in twain, and passed between the parts thereof;
19 Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
even the princes of Judah, and the princes of Jerusalem, the eunuchs and the priests, and all the people of the land, —who passed between the parts of the calf,
20 zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
yea I will give them into the hand of their enemies, and into the hand of them who are seeking their life, —and their dead bodies shall become food for the birds of the heavens, and for the beasts of the earth.
21 “Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
Zedekiah king of Judah also with his princes, will I give into the hand of their enemies, and into the hand of them who are seeking their life, —even into the hand of the force of the king of Babylon, who are going up from you.
22 Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”
Behold me! giving command, Declareth Yahweh, and I will bring them back unto this city, and they will fight against it and capture it, and consume it with fire, —and, the cities of Judah, will I make too desolate to have an inhabitant.