< Irmiya 34 >

1 Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
The word that came to Jeremias from the Lord, (when Nabuchodonosor king of Babylon, and all his army, and all the kingdoms of the earth, that were under the power of his hand, and all the people fought against Jerusalem and against all the cities thereof, ) saying:
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
Thus saith the Lord, the God of Israel: Go, and speak to Sedecias king of Juda, and say to him: Thus saith the Lord: Behold I will deliver this city into the hands of the king of Babylon, and he shall burn it with fire.
3 Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
And thou shalt not escape out of his hand: but thou shalt surely be taken, and thou shalt be delivered into his hand: and thy eyes shall see the eyes of the king of Babylon, and his mouth shall speak with thy mouth, and thou shalt go to Babylon.
4 “‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
Yet hear the word of the Lord, O Sedecias king of Juda: Thus saith the Lord to thee: Thou shalt not die by the sword.
5 za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
But thou shalt die in peace, and according to the burnings of thy fathers, the former kings that were before thee, so shall they burn thee: and they shall mourn for thee, saying: Alas, Lord: for I have spoken the word, saith the Lord.
6 Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
And Jeremias the prophet spoke all these words to Sedecias the king of Juda in Jerusalem.
7 yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
And the army of the king of Babylon fought against Jerusalem, and against all the cities of Juda that were left, against Lachis, and against Azecha: for these remained of the cities of Juda, fenced cities.
8 Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
The word that came to Jeremias from the Lord, after that king Sedecias had made a covenant with all the people in Jerusalem making a proclamation:
9 Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
That every man should let his manservant, and every man his maidservant, being a Hebrew man or a Hebrew woman, go free: and that they should not lord it over them, to wit, over the Jews their brethren.
10 Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
And all the princes, and all the people who entered into the covenant, heard that every man should let his manservant, and every man his maidservant go free, and should no more have dominion over them: and they obeyed, and let them go free.
11 Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
But afterwards they turned: and brought back again their servants and their handmaids, whom they had let go free, and brought them into subjection as menservants and maidservants.
12 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
And the word of the Lord came to Jeremias from the Lord, saying:
13 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
Thus saith the Lord the God of Israel: I made a covenant with your fathers in the day that I brought them out of the land of Egypt, out of the house of bondage, saying:
14 ‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
At the end of seven years, let ye go every man his brother being a Hebrew, who hath been sold to thee, so he shall serve thee six years: and thou shalt let him go free from thee: and your fathers did not hearken to me, nor did they incline their ear.
15 Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
And you turned today, and did that which was right in my eyes, in proclaiming liberty every one to his brother: and you made a covenant in my sight, in the house upon which my name is invocated.
16 Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
And you are fallen back, and have defiled my name: and you have brought back again every man his manservant, and every man his maidservant, whom you had let go free, and set at liberty: and you have brought them into subjection to be your servants and handmaids.
17 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
Therefore thus saith the Lord: You have not hearkened to me, in proclaiming liberty every man to his brother and every man to his friend: behold I proclaim a liberty for you, saith the Lord, to the sword, to the pestilence, and to the famine: and I will cause you to be removed to all the kingdoms of the earth.
18 Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
And I will give the men that have transgressed my covenant, and have not performed the words of the covenant which they agreed to in my presence, when they cut the calf in two and passed between the parts thereof:
19 Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
The princes of Juda, and the princes of Jerusalem, the eunuchs, and the priests, and all the people of the land that passed between the parts of the calf:
20 zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
And I will give them into the hands of their enemies, and into the hands of them that seek their life: and their dead bodies shall be for meat to the fowls of the air, and to the beasts of the earth.
21 “Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
And Sedecias the king of Juda, and his princes, I will give into the hands of their enemies, and into the hands of them that seek their lives, and into the hands of the armies of the king of Babylon, which are gone from you.
22 Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”
Behold I will command, saith the Lord, and I will bring them again to this city, and they shall fight against it, and take it, and burn it with fire: and I will make the cities of Juda a desolation, without an inhabitant.

< Irmiya 34 >