< Irmiya 33 >

1 Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
Além disso, a palavra de Javé veio a Jeremias pela segunda vez, enquanto ele ainda estava preso no tribunal da guarda, dizendo:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
“Javé que o faz, Javé que o forma para estabelecê-lo - Javé é seu nome, diz:
3 ‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
'Chame-me, e eu lhe responderei, e lhe mostrarei coisas grandes e difíceis, que você não sabe”.
4 Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
Para Javé, o Deus de Israel, diz sobre as casas desta cidade e sobre as casas dos reis de Judá, que são derrubadas para fazer uma defesa contra os montes e contra a espada:
5 a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
'Enquanto os homens vêm para lutar com os caldeus, e para enchê-los de cadáveres de homens, que matei em minha ira e em minha ira, e por todos cuja maldade escondi o meu rosto desta cidade,
6 “‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
eis que lhe trarei saúde e cura, e os curarei; e lhes revelarei abundância de paz e de verdade.
7 Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
restaurarei as fortunas de Judá e Israel, e as construirei como no início.
8 Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
Vou limpá-los de toda sua iniqüidade pela qual pecaram contra mim. Perdoarei todas as suas iniqüidades pelas quais pecaram contra mim e pelas quais transgrediram contra mim.
9 Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
Esta cidade será para mim um nome de alegria, de louvor e de glória, diante de todas as nações da terra, que ouvirão todo o bem que lhes faço, e temerão e tremerão por todo o bem e por toda a paz que eu lhe forneço”.
10 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
diz Yahweh: “Mais uma vez será ouvido neste lugar, sobre o qual vocês dizem: 'É desperdício, sem homem e sem animal, mesmo nas cidades de Judá, e nas ruas de Jerusalém, que estão desoladas, sem homem e sem habitante e sem animal',
11 sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
a voz da alegria e a voz da alegria, a voz do noivo e a voz da noiva, a voz daqueles que dizem: 'Dê graças a Javé dos Exércitos, pois Javé é bom, pois sua bondade amorosa perdura para sempre';”que trazem a ação de graças à casa de Iavé”. Pois eu farei com que o cativeiro da terra seja revertido como no início”, diz Javé.
12 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
Yahweh dos Exércitos diz: “Mais uma vez haverá neste lugar, que é um desperdício, sem homem e sem animal, e em todas as suas cidades, uma habitação de pastores que faz com que seus rebanhos se deitem.
13 A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
Nas cidades da região montanhosa, nas cidades da planície, nas cidades do Sul, na terra de Benjamim, nos lugares ao redor de Jerusalém, e nas cidades de Judá, os rebanhos passarão novamente sob as mãos daquele que os conta”, diz Yahweh.
14 “‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
“Eis que vêm os dias”, diz Javé, “em que cumprirei a boa palavra que disse sobre a casa de Israel e sobre a casa de Judá”.
15 “‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
“Naqueles dias e naquela época, Vou fazer crescer um ramo de retidão até David. Ele executará a justiça e a retidão na terra.
16 A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
Nesses dias, Judah será salvo, e Jerusalém habitará em segurança. Este é o nome pelo qual ela será chamada: Yahweh nossa retidão”.
17 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
Para Yahweh diz: “Nunca faltará a David um homem para sentar-se no trono da casa de Israel.
18 ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
Os sacerdotes levíticos não faltará um homem diante de mim para oferecer holocaustos, para queimar ofertas de refeições e para fazer sacrifícios continuamente”.
19 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
A palavra de Javé veio a Jeremias, dizendo:
20 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
“Javé diz: 'Se você puder quebrar meu pacto do dia e meu pacto da noite, para que não haja dia e noite no tempo deles,
21 to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
então meu pacto também poderá ser quebrado com David, meu servo, para que ele não tenha um filho para reinar em seu trono; e com os sacerdotes levíticos, meus ministros.
22 Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
Como o exército do céu não pode ser contado, e a areia do mar não pode ser medida, assim multiplicarei a prole de Davi, meu servo, e os levitas que ministram a mim”.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
A palavra de Javé veio a Jeremias, dizendo:
24 “Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
“Não considere o que este povo falou, dizendo: “Javé expulsou as duas famílias que ele escolheu? Assim eles desprezam meu povo, que não deve mais ser uma nação diante deles”.
25 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
Yahweh diz: “Se minha aliança do dia e da noite falhar, se eu não tiver nomeado as ordenanças do céu e da terra,
26 to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”
então também lançarei fora a descendência de Jacó, e de Davi meu servo, para que eu não tome de sua descendência para ser governante sobre a descendência de Abraão, Isaac e Jacó; pois farei com que o cativeiro deles seja revertido e terei misericórdia deles”.

< Irmiya 33 >