< Irmiya 33 >
1 Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
Og Herrens ord kom til Jeremias annen gang, mens han ennu satt fengslet i vaktgården, og det lød så:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
Så sier Herren, som gjør det han vil, Herren som uttenker det for også å fullføre det, han hvis navn er Herren:
3 ‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
Rop til mig, og jeg vil svare dig, og jeg vil forkynne dig store og ufattelige ting, ting som du ikke kjenner.
4 Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
For så sier Herren, Israels Gud, om husene i denne by og om husene til Judas konge, som er revet ned til forsvar mot fiendens voller og sverd:
5 a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
De kommer for å stride mot kaldeerne; men det blir bare til å fylle husene med døde kropper av de menn som jeg slår i min vrede og harme, og som ved sin store ondskap har voldt at jeg har skjult mitt åsyn for denne by.
6 “‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
Se, jeg legger forbinding og lægedom på den og læger dem, og jeg vil la dem se en overflod av fred og trygghet.
7 Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
Og jeg vil gjøre ende på Judas fangenskap og Israels fangenskap, og jeg vil bygge dem op som i den første tid.
8 Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
Og jeg vil rense dem fra all deres misgjerning, hvormed de har syndet mot mig, og jeg vil forlate alle deres misgjerninger, hvormed de har syndet og forbrutt sig mot mig.
9 Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
Og byen skal være mig til et gledesnavn, til pris og pryd for alle jordens folkeslag, når de får høre om alt det gode jeg gjør imot den, og de skal skjelve og beve når de får se alt det gode og all den fred jeg gir den.
10 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
Så sier Herren: På dette sted om hvilket I sier: Det er øde, uten mennesker og uten fe - her i Judas byer og på Jerusalems gater, som ligger øde, uten mennesker og uten innbyggere og uten fe, skal det ennu en gang høres
11 sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
fryds røst og gledes røst, brudgoms røst og bruds røst, rop av dem som sier: Lov Herren, hærskarenes Gud, for Herren er god, hans miskunnhet varer evindelig - dem som bærer frem takkoffer i Herrens hus. For jeg vil gjøre ende på fangenskapet, så landet blir som i den første tid, sier Herren.
12 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
Så sier Herren, hærskarenes Gud: Ennu en gang skal det på dette sted som er øde, både uten mennesker og uten fe, og i alle dets byer være et tilhold for hyrder som lar fårene hvile der.
13 A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
I byene i fjellbygdene, i byene i lavlandet og i byene i sydlandet og i Benjamins land og i landet omkring Jerusalem og i Judas byer skal fårene ennu en gang gå forbi den som teller dem, sier Herren.
14 “‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Se, dager kommer, sier Herren, da jeg vil opfylle det gode ord jeg har talt om Israels hus og om Judas hus.
15 “‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
I de dager og på den tid vil jeg la spire frem for David en rettferdig spire, og han skal gjøre rett og rettferdighet i landet.
16 A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
I de dager skal Juda bli frelst og Jerusalem bo trygt, og dette er det navn det skal kalles med: Herren, vår rettferdighet.
17 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
For så sier Herren: Det skal aldri fattes en mann av Davids ætt som skal sitte på Israels trone,
18 ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
og av de levittiske presters ætt skal det aldri fattes en mann for mitt åsyn som ofrer brennoffer og brenner matoffer og bærer frem slaktoffer alle dager.
19 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Og Herrens ord kom til Jeremias, og det lød så:
20 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
Så sier Herren: Dersom I kan bryte min pakt med dagen og min pakt med natten, så det ikke blir dag og natt i sin tid,
21 to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
da skal også min pakt med min tjener David bli brutt, så han ikke får nogen sønn som blir konge og sitter på hans trone, og min pakt med mine tjenere de levittiske prester.
22 Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
Likesom himmelens hær ikke kan telles og havets sand ikke måles, således vil jeg gjøre min tjener Davids ætt og levittene som tjener mig, tallrike.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Og Herrens ord kom til Jeremias, og det lød så:
24 “Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
Har du ikke gitt akt på hvad dette folk har talt og sagt: De to slekter som Herren hadde utvalgt, dem forkastet han? Og mitt folk forakter de, så det ikke mere er noget folk i deres øine.
25 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
Så sier Herren: Dersom jeg ikke har oprettet min pakt med dag og natt, ikke gitt lover for himmel og jord,
26 to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”
så vil jeg også forkaste Jakobs og min tjener Davids ætt, så jeg ikke av hans ætt tar nogen til å herske over Abrahams, Isaks og Jakobs ætt; for jeg vil gjøre ende på deres fangenskap og forbarme mig over dem.