< Irmiya 33 >

1 Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie une seconde fois, lorsqu’il était encore enfermé dans le vestibule de la prison, disant:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
Voici ce que dit le Seigneur, qui doit faire, et disposer, et préparer cela; le Seigneur est son nom.
3 ‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
Crie vers moi, et je t’exaucerai, et je t’annoncerai des choses grandes et certaines que tu ne sais pas.
4 Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
Parce que voici ce que dit le Seigneur, Dieu d’Israël, aux maisons de cette ville et aux maisons du roi de Juda qui ont été détruites, et aux fortifications et au glaive
5 a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
De ceux qui viennent, afin de combattre contre les Chaldéens, et afin de les remplir des cadavres des hommes que j’ai frappés dans ma fureur et dans mon indignation, détournant ma face de cette cité à cause de toute leur malice:
6 “‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
Voici que moi, je refermerai leur cicatrice, je leur donnerai la santé et je les soignerai; et je leur montrerai la paix et la vérité qu’ils demandent.
7 Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
Et je ferai retourner certainement Juda et Jérusalem; et je les établirai comme dès le commencement.
8 Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
Et je les purifierai de toute leur iniquité par laquelle ils ont péché contre moi, et je leur pardonnerai toutes leurs iniquités par lesquelles ils se sont rendus coupables envers moi, et m’ont méprisé.
9 Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
Ce sera pour moi un renom, et une joie, et une louange, et une exultation parmi toutes les nations de la terre, qui apprendront tous les biens que moi je dois leur faire; et elles auront peur et elles seront troublées à cause de tous les biens et de toute la paix que moi je leur accorderai.
10 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
Voici ce que dit le Seigneur: On entendra encore dans ce lieu (que vous dites être un désert, parce qu’il n’y a pas d’homme ni de bête, dans les cités de Juda et au dehors de Jérusalem, cités qui sont désolées, sans homme et sans habitant, et sans troupeau)
11 sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
La voix de la joie et la voix de l’allégresse, la voix de l’époux et la voix de l’épouse, la voix de ceux qui diront: Louez le Seigneur des armées parce que bon est le Seigneur, parce qu’éternelle est sa miséricorde, et la voix de ceux qui portent des vœux dans la maison du Seigneur; car je ramènerai les captifs de cette terre, et je les rétablirai comme dès le commencement, dit le Seigneur.
12 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Il y aura encore dans ce lieu désert, sans homme et sans bête, et dans toutes ses cités, une demeure de pasteurs qui feront reposer des troupeaux.
13 A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
Dans les cités des montagnes, et dans les cités de la plaine, et dans les cités qui sont au midi, et dans la terre de Benjamin, et dans les environs de Jérusalem, et dans les cités de Juda, les troupeaux passeront encore sous la main de celui qui les compte, dit le Seigneur.
14 “‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Voilà que des jours viennent, dit le Seigneur, et je réaliserai la bonne parole que j’ai dite à la maison d’Israël et à la maison de Juda.
15 “‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
En ces jours-là et en ce temps-là, je ferai germer dans David un germe de justice; et il rendra le jugement et la justice sur la terre.
16 A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
En ces jours-là, Juda sera sauvé, et Jérusalem habitera en assurance; et voici le nom dont ils l’appelleront: Le Seigneur notre juste.
17 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
Car voici ce que dit le Seigneur: Il ne manquera pas dans la race de David, d’homme qui s’asseye sur le trône de la maison d’Israël.
18 ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
Et d’entre les prêtres et d’entre les Lévites, il ne manquera pas un homme devant ma face qui offre des holocaustes, allume le sacrifice, et tue des victimes, tous les jours.
19 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie, disant:
20 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
Voici ce que dit le Seigneur: Si mon alliance avec le jour et mon alliance avec la nuit peuvent être rendues vaines, en sorte qu’il n’y ait pas de jour et de nuit en leurs temps,
21 to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
Mon alliance avec David, mon serviteur, pourra aussi être vaine, en sorte qu’il n’y ait pas de lui un fils qui règne sur son trône, ni de Lévites et de prêtres qui soient mes ministres.
22 Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
Comme les étoiles du ciel ne peuvent être comptées, ni le sable de la mer être mesuré, ainsi je multiplierai la race de David, mon serviteur, et les Lévites, mes ministres.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie, disant:
24 “Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
Est-ce que tu n’as pas vu comment a parlé ce peuple, disant: Les deux familles qu’avait choisies le Seigneur ont été rejetées; et ils ont méprisé mon peuple, parce qu’il n’est plus une nation devant eux?
25 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
Voici ce que dit le Seigneur: Si je n’ai pas établi mon alliance entre le jour et la nuit, et des lois pour le ciel et pour la terre,
26 to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”
Certainement, je rejetterai aussi la race de Jacob et de David, mes serviteurs, afin de ne pas prendre de leur race des princes de la race d’Abraham, d’Isaac et de Jacob; car je ramènerai leurs captifs, et j’aurai pitié d’eux.

< Irmiya 33 >