< Irmiya 33 >

1 Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
Et la parole de l'Eternel fut [adressée] une seconde fois à Jérémie, quand il était encore enfermé dans la cour de la prison, en disant:
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
Ainsi a dit l'Eternel qui s'en va faire ceci, l'Eternel qui s'en va le former pour l'établir, le Nom duquel est l'Eternel.
3 ‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
Crie vers moi, je te répondrai, et je te déclarerai des choses grandes et cachées, lesquelles tu ne sais point.
4 Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
Car ainsi a dit l'Eternel, le Dieu d'Israël, touchant les maisons de cette ville-ci, et les maisons des Rois de Juda; elles s'en vont être démolies par le moyen des terrasses, et par l'épée.
5 a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
Ils sont venus à combattre contre les Caldéens, mais ç'a été pour remplir leurs maisons des corps morts des hommes que j'ai fait frapper en ma colère et en ma fureur, et parce que j'ai caché ma face de cette ville à cause de toute leur malice.
6 “‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
Voici, je m'en vais lui donner la santé et la guérison, je les guérirai, et je leur ferai voir abondance de paix et de vérité.
7 Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
Et je ferai retourner les captifs de Juda, et les captifs d'Israël, et je les rétablirai comme auparavant.
8 Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
Et je les purifierai de toute leur iniquité, par laquelle ils ont péché contre moi; et je pardonnerai toutes leurs iniquités par lesquelles ils ont péché contre moi, et par lesquelles ils ont péché grièvement contre moi.
9 Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
Et [cette ville] me sera un sujet de réjouissance, de louange et de gloire, chez toutes les nations de la terre qui entendront parler de tout le bien que je vais leur faire, et elles seront effrayées et épouvantées à cause de tout le bien, et de toute la prospérité que je vais lui donner.
10 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
Ainsi a dit l'Eternel: dans ce lieu-ci duquel vous dites: il est désert, n'y ayant ni homme ni bête, dans les villes de Juda, et dans les rues de Jérusalem, qui sont désolées, n'y ayant ni homme, ni habitant, ni aucune bête, on y entendra encore,
11 sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
La voix de joie, et la voix d'allégresse, la voix de l'époux, et la voix de l'épouse, [et] la voix de ceux qui disent: célébrez l'Eternel des armées; car l'Eternel est bon, parce que sa miséricorde demeure à toujours, lorsqu'ils apportent des oblations d'action de grâces à la maison de l'Eternel; car je ferai retourner les captifs de ce pays, [et je les mettrai] au même état qu'auparavant, a dit l'Eternel.
12 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
Ainsi a dit l'Eternel des armées: en ce lieu désert, où il n'y a ni homme ni bête, et dans toutes ses villes, il y aura encore des cabanes de bergers qui y feront reposer leurs troupeaux;
13 A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
Dans les villes des montagnes, et dans les villes de la plaine, dans les villes du Midi, dans le pays de Benjamin, dans les environs de Jérusalem, et dans les villes de Juda; et les troupeaux passeront encore sous les mains de celui qui les compte, a dit l'Eternel.
14 “‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Voici, les jours viennent, dit l'Eternel, que je mettrai en effet la bonne parole que j'ai prononcée touchant la maison d'Israël, et la maison de Juda.
15 “‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
En ces jours-là, et en ce temps-là je ferai germer à David le Germe de justice, qui exercera le jugement et la justice en la terre.
16 A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
En ces jours-là Juda sera délivré, et Jérusalem habitera en assurance, et c'est ici le nom dont elle sera appelée: l'Eternel notre justice.
17 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
Car ainsi a dit l'Eternel, il ne manquera jamais à David d'homme assis sur le trône de la maison d'Israël;
18 ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
Et d'entre les Sacrificateurs Lévites, il ne manquera jamais d'y avoir devant moi d'homme offrant des holocaustes, faisant les parfums de gâteau, et faisant des sacrifices tous les jours.
19 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Davantage la parole de l'Eternel fut [adressée] à Jérémie, en disant:
20 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
Ainsi a dit l'Eternel: Si vous pouvez abolir mon alliance touchant le jour, et mon alliance touchant la nuit, tellement que le jour et la nuit ne soient plus en leur temps;
21 to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
Aussi mon alliance avec David mon serviteur sera abolie; tellement qu'il n'ait plus de fils régnant sur son trône; et avec les Lévites Sacrificateurs, faisant mon service.
22 Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
Car [comme] on ne peut compter l'armée des cieux, ni mesurer le sable de la mer, ainsi je multiplierai la postérité de David mon serviteur, et les Lévites qui font mon service.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
La parole de l'Eternel fut encore [adressée] à Jérémie, en disant:
24 “Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
N'as-tu pas vu ce que ce peuple a prononcé, disant: l'Eternel a rejeté les deux familles qu'il avait élues; car [par là] ils méprisent mon peuple; tellement qu'à leur compte il ne sera plus une nation?
25 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
Ainsi a dit l'Eternel: si [je n'ai point établi] mon alliance touchant le jour et la nuit, et si je n'ai point établi les ordonnances des cieux et de la terre;
26 to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”
Aussi rejetterai-je la postérité de Jacob, et celle de David mon serviteur, pour ne prendre plus de sa postérité des gens qui dominent sur la postérité d'Abraham, d'Isaac, et de Jacob; car je ferai retourner leurs captifs, et j'aurai compassion d'eux.

< Irmiya 33 >