< Irmiya 33 >

1 Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
The word of Jehovah came also to Jeremiah the second time, while he was shut up in the court of the prison, and said: —
2 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
Thus saith Jehovah, who doeth it, Jehovah who disposeth it, to establish it; Jehovah is his name.
3 ‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
Call to me, and I will answer thee, And I will show thee great things, And hidden things which thou knowest not.
4 Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
For thus saith Jehovah, the God of Israel, Concerning the houses of this city, And concerning the houses of the kings of Judah, Which are thrown down toward the mounds and the sword,
5 a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
To fight with the Chaldaeans, And to fill them with the dead bodies of men, Whom I have smitten in mine anger and in my wrath, And for all whose wickedness I have hid my face from this city:
6 “‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
Behold, I will bind up her wounds, and heal them, And I will reveal to them abundance of peace and stability.
7 Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
And I will bring back the captives of Judah, And the captives of Israel, And I will build them, as at the first.
8 Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
And I will cleanse them from all their iniquity, Whereby they have sinned against me; And I will forgive all their iniquities, Whereby they have sinned, And have rebelled against me.
9 Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
And it [[the city]] shall be to me a name of joy, A praise and a glory among all the nations of the earth, Who shall hear of all the good which I do to them. And they shall fear and tremble because of all the good, And because of all the prosperity, which I bestow upon it.
10 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
Thus saith Jehovah: Yet again shall be heard in this place, Of which ye say, “It is desolate, without man and without beast,” In the cities of Judah, and in the streets of Jerusalem, Which are desolate, without man, Even without an inhabitant and without beast,
11 sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
The voice of joy and the voice of gladness, The voice of the bridegroom and the voice of the bride, The voice of them that say, “Praise ye Jehovah of hosts, For Jehovah is good, For his mercy endureth forever!” And of them that bring an offering of praise to the house of Jehovah. For I will restore the captives of the land, As at the first, saith Jehovah.
12 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
Thus saith Jehovah of hosts: Yet again shall there be in this place, Which is desolate, without man and without beast, And in all the cities thereof, A habitation of shepherds, who shall cause their flocks to rest;
13 A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
In the cities of the hill-country, and in the cities of the plain, And in the cities of the south, and in the land of Benjamin, And in the places about Jerusalem, and in the cities of Judah, Shall the flocks pass yet again Under the hands of him that numbereth them, saith Jehovah.
14 “‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Behold, the days come, saith Jehovah, That I will perform that good thing Which I have spoken concerning the house of Israel, And concerning the house of Judah.
15 “‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
In those days and at that time Will I cause to grow up from David a righteous branch, Who shall maintain justice and equity in the land.
16 A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
In those days shall Judah be saved, And Jerusalem shall dwell securely; And this is the name which shall be given her, Jehovah-is-our-salvation.
17 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
For thus saith Jehovah: There shall never fail from David A man to sit upon the throne of the house of Israel;
18 ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
Neither from the priests and the Levites Shall a man fail before me, To offer burnt-offerings, and to kindle meat-offerings, And to perform sacrifice continually.
19 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
And the word of Jehovah came to Jeremiah and said,
20 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
Thus saith Jehovah: If ye can break my covenant concerning the day, And my covenant concerning the night, So that there shall no more be day and night in their season,
21 to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
Then also may my covenant with David my servant be broken, So that he shall not have a son to reign upon his throne, And with the Levites, the priests, my servants.
22 Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
As the host of heaven cannot be numbered, Nor the sand of the sea measured, So will I multiply the posterity of David my servant, And the Levites who minister to me.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
The word of Jehovah came also to Jeremiah, saying:
24 “Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
Seest thou not what this people speaketh, saying, “The two families, which Jehovah chose, he hath cast off”? Therefore they despise my people, So that they are no more a people in their eyes.
25 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
Thus saith Jehovah: If my covenant concerning the day and the night be not maintained, And if I have not established the ordinances of the heaven and the earth,
26 to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”
Then will I cast away the posterity of Jacob, and of David, my servant, So as not to take of his posterity to be rulers Over the posterity of Abraham, Isaac, and Jacob; For I will bring them back from their captivity, And have mercy upon them.

< Irmiya 33 >