< Irmiya 32 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
Pada tahun kesepuluh pemerintahan Zedekia raja Yehuda, yaitu tahun kedelapan belas pemerintahan Nebukadnezar raja Babel, TUHAN berbicara kepadaku.
2 Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
Pada waktu itu tentara raja Babel sedang menyerang Yerusalem. Aku ditahan di pelataran istana raja
3 Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
oleh Raja Zedekia karena dituduh telah mengumumkan bahwa TUHAN berkata begini, "Raja Babel akan Kubiarkan menaklukkan dan menduduki kota ini,
4 Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
dan Raja Zedekia tidak akan luput. Ia akan diserahkan kepada raja Babel, dan menghadap raja itu serta berbicara sendiri dengan dia.
5 Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
Kemudian Zedekia akan diangkut ke Babel dan tinggal di sana sampai Aku menghukum dia. Sekalipun ia memerangi orang Babel, ia tidak akan berhasil. Aku, TUHAN, telah berbicara."
6 Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
TUHAN berkata kepadaku
7 Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
bahwa Hanameel, anak laki-laki pamanku Salum, akan datang untuk minta supaya aku membeli tanahnya di Anatot di wilayah Benyamin. Sebab, akulah sanaknya yang terdekat yang berhak membeli tanah itu.
8 “Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
Lalu tepat seperti yang telah dikatakan TUHAN, datanglah Hanameel kepadaku di pelataran istana, dan minta supaya aku membeli tanahnya. Karena itu aku yakin TUHAN betul-betul telah berbicara kepadaku.
9 saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
Maka aku membeli tanah itu dari Hanameel dengan harga tujuh belas uang perak. Kupanggil saksi-saksi dan di depan mereka kutandatangani surat pembeliannya, lalu kububuhi segel dan kutimbang uangnya.
10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
11 Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
Kemudian aku mengambil surat pembelian itu yang sudah diberi segel dan berisi syarat-syarat serta ketentuan-ketentuan. Kuambil juga salinan surat yang tidak ada segelnya,
12 na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
dan kedua surat itu kuberikan kepada Barukh anak Neria cucu Mahseya. Aku menyerahkannya di depan Hanameel serta saksi-saksi yang telah menandatangani surat-surat itu, dan di depan orang-orang yang sedang duduk di pelataran itu.
13 “A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
Di depan mereka semua aku berkata kepada Barukh,
14 ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
"TUHAN Yang Mahakuasa, Allah Israel, memerintahkan supaya engkau mengambil kedua surat ini, baik yang asli maupun salinannya, dan memasukkannya ke dalam sebuah periuk tembikar supaya tahan lama.
15 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
TUHAN Yang Mahakuasa, Allah Israel, berkata bahwa rumah, tanah, dan kebun anggur kelak akan diperjualbelikan lagi di negeri ini."
16 “Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
Setelah surat-surat pembelian itu kuberikan kepada Barukh, aku berdoa,
17 “A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
"TUHAN Yang Mahatinggi, Engkaulah yang menciptakan langit dan bumi dengan kuasa dan kemampuan-Mu yang besar. Tak ada sesuatu pun yang sukar bagi-Mu.
18 Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
Engkau menunjukkan kasih-Mu yang abadi kepada beribu-ribu orang, tapi Engkau juga menghukum orang karena dosa orang tuanya. Engkau Allah yang agung dan perkasa; nama-Mu TUHAN Yang Mahakuasa.
19 manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
Rencana-rencana-Mu hebat, dan perbuatan-perbuatan-Mu ajaib; Engkau melihat segala yang dilakukan manusia, dan membalas mereka sesuai dengan perbuatan mereka.
20 Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
Dahulu kala Engkau melakukan keajaiban dan hal-hal luar biasa di Mesir, dan sampai sekarang pun Engkau masih terus melakukannya, baik di antara orang Israel maupun di antara segala bangsa lain. Karena itu kini Engkau termasyhur di mana-mana.
21 Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
Dengan kuasa dan kekuatan-Mu yang besar Engkau membawa umat Israel keluar dari Mesir. Engkau melakukan mujizat-mujizat dan keajaiban-keajaiban serta kejadian-kejadian yang menggemparkan musuh.
22 Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
Negeri yang baik dan subur ini Kauberikan kepada mereka seperti yang telah Kaujanjikan kepada leluhur mereka.
23 Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
Tapi ketika mereka datang ke negeri ini dan merebutnya, mereka tidak taat kepada perintah-perintah-Mu, dan tidak hidup menurut ajaran-ajaran-Mu. Semua yang Kauperintahkan kepada mereka tidak satu pun yang mereka laksanakan. Sebab itu Engkau mendatangkan segala bencana ini ke atas mereka.
24 “Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
Orang-orang Babel telah membangun tembok-tembok pengepungan di sekeliling kota untuk merebutnya, dan sekarang mereka menyerang. Pertempuran, kelaparan, dan wabah penyakit akan menyebabkan kota ini jatuh ke tangan mereka. Engkau melihat bahwa semua yang Kaukatakan telah menjadi kenyataan.
25 Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
Namun demikian, ya TUHAN Yang Mahatinggi, Engkaulah yang menyuruh aku membeli tanah ini di depan saksi-saksi, sekali pun sebentar lagi kota akan direbut oleh orang Babel."
26 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Kemudian TUHAN berkata kepadaku,
27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
"Akulah TUHAN, Allah semua orang. Tak ada yang sulit bagi-Ku.
28 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
Kota ini akan Kubiarkan dikuasai oleh Nebukadnezar raja Babel bersama pasukannya. Mereka akan merebut kota ini,
29 Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
dan membakarnya sampai habis bersama-sama dengan rumah-rumah di mana orang menimbulkan kemarahan-Ku, karena di atas atap rumah-rumah itu mereka membakar dupa kepada Baal dan menuangkan anggur untuk persembahan bagi dewa-dewa.
30 “Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
Sejak permulaan sejarah mereka, orang Israel dan orang Yehuda telah membuat Aku tidak senang. Mereka membangkitkan kemarahan-Ku dengan perbuatan-perbuatan mereka yang jahat.
31 Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
Sejak kota ini dibangun, penduduknya telah membuat Aku marah sekali. Aku telah memutuskan untuk membinasakannya,
32 Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
karena segala kejahatan yang dilakukan orang Yehuda dan Yerusalem bersama para raja, pejabat pemerintah, imam, dan nabi-nabi mereka.
33 Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
Mereka telah meninggalkan Aku dan sekali pun Aku terus mengajar mereka, mereka tidak mau mendengarkan dan tidak mau insaf.
34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
Malah rumah yang dibangun untuk tempat ibadat kepada-Ku telah dinajiskan oleh mereka dengan meletakkan berhala-berhala mereka yang memuakkan di tempat itu.
35 Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
Mereka membangun mezbah-mezbah untuk Baal di Lembah Hinom, dan mempersembahkan anak-anak mereka kepada Dewa Molokh. Padahal, Aku tak pernah menyuruh mereka melakukan hal itu, bahkan tak pernah timbul dalam pikiran-Ku bahwa mereka akan melakukan perbuatan sekeji itu dan membuat orang Yehuda berdosa."
36 “Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
TUHAN, Allah Israel, berkata kepadaku, "Yeremia, bangsa Israel berkata bahwa peperangan, kelaparan, dan wabah penyakit akan membuat kota ini jatuh ke tangan raja Babel. Sekarang, dengarkan juga apa yang akan Kukatakan.
37 tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
Aku akan mengumpulkan bangsa ini dari semua negeri tempat mereka Kuceraiberaikan karena kemarahan-Ku dan geram-Ku kepada mereka. Mereka akan Kubawa kembali ke tempat ini dan Kumungkinkan tinggal di sini dengan aman.
38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
Mereka akan menjadi umat-Ku, dan Aku menjadi Allah mereka.
39 Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
Aku akan memberi mereka hanya satu tujuan hidup: yaitu, menghormati Aku selama-lamanya; hal itu akan membawa kebaikan bagi mereka sendiri, dan bagi keturunan mereka.
40 Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
Aku akan membuat perjanjian yang kekal dengan mereka. Aku tak akan berhenti berbuat baik kepada mereka. Aku akan membuat mereka takut dan hormat kepada-Ku dengan sepenuh hati supaya mereka tidak menjauhi Aku.
41 Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
Aku akan senang berbuat baik kepada mereka, dan membuat mereka menetap di negeri ini untuk selama-lamanya.
42 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
Sebagaimana Aku telah mendatangkan bencana ke atas bangsa ini, begitu pula Aku akan memberikan semua yang baik yang telah Kujanjikan kepada mereka.
43 Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
Orang berkata bahwa negeri ini telah menjadi seperti padang gurun yang tidak didiami oleh manusia dan binatang, dan bahwa negeri ini telah jatuh ke tangan orang Babel. Tapi Aku berkata bahwa kelak ladang-ladang akan diperjualbelikan lagi di negeri ini;
44 Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
surat pembeliannya akan ditandatangani, disegel, dan diperkuat oleh saksi-saksi. Itu akan terjadi di wilayah Benyamin, di desa-desa sekitar Yerusalem, di kota-kota Yehuda, di kota-kota di daerah pegunungan, di daerah kaki pegunungan, dan di Yehuda selatan. Bangsa ini akan Kupulihkan keadaannya di negeri ini. Aku, TUHAN, telah berbicara."

< Irmiya 32 >