< Irmiya 32 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
La parole qui fut adressée par l'Éternel à Jérémie, la dixième année de Sédécias, roi de Juda; c'était l'an dix-huitième de Nébucadnetsar.
2 Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
L'armée du roi de Babylone assiégeait alors Jérusalem, et Jérémie, le prophète, était enfermé dans la cour de la prison qui était dans la maison du roi de Juda.
3 Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
Sédécias, roi de Juda, l'avait fait enfermer, et lui avait dit: Pourquoi prophétises-tu, en disant: Ainsi a dit l'Éternel: Voici, je vais livrer cette ville entre les mains du roi de Babylone, et il la prendra;
4 Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
Et Sédécias, roi de Juda, n'échappera pas aux mains des Caldéens; mais il sera certainement livré aux mains du roi de Babylone, et il lui parlera bouche à bouche, et ses yeux verront ses yeux;
5 Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
Et il emmènera Sédécias à Babylone, et il sera là jusqu'à ce que je le visite, dit l'Éternel. Quand vous combattrez contre les Caldéens, vous ne réussirez pas.
6 Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Alors Jérémie dit: La parole de l'Éternel m'a été adressée en ces termes:
7 Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
Voici Hanaméel, fils de Shallum, ton oncle, qui vient vers toi pour te dire: Achète mon champ qui est à Anathoth; car tu as le droit de rachat pour l'acquérir.
8 “Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
Et Hanaméel, fils de mon oncle, vint vers moi, selon la parole de l'Éternel, dans la cour de la prison, et il me dit: Achète, je te prie, mon champ qui est à Anathoth, au pays de Benjamin, car tu as le droit d'héritage et de rachat; achète-le. Et je connus que c'était la parole de l'Éternel.
9 saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
Ainsi j'achetai de Hanaméel, fils de mon oncle, le champ d'Anathoth, et je lui pesai l'argent: dix-sept sicles d'argent.
10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
Puis j'écrivis un contrat, que je cachetai; et je pris des témoins et pesai l'argent dans la balance.
11 Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
Je pris ensuite le contrat, tant celui qui était cacheté, selon l'ordonnance et les statuts, que celui qui était ouvert.
12 na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
Et je remis le contrat d'acquisition à Baruc, fils de Nérija, fils de Machséja, en présence de Hanaméel, fils de mon oncle, et des témoins qui avaient signé le contrat d'acquisition, et en présence de tous les Juifs qui étaient assis dans la cour de la prison.
13 “A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
Et je donnai cet ordre à Baruc, en leur présence:
14 ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
Ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël: Prends ces écrits, ce contrat d'acquisition, celui qui est cacheté et celui qui est ouvert, et mets-les dans un vase de terre, afin qu'ils puissent se conserver longtemps.
15 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
Car ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël: On achètera encore des maisons, des champs et des vignes dans ce pays.
16 “Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
Et après que j'eus remis à Baruc, fils de Nérija, le contrat d'acquisition, je fis ma prière à l'Éternel, en disant:
17 “A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
Ah! Seigneur Éternel! voici, tu as fait le ciel et la terre, par ta grande puissance et par ton bras étendu: aucune chose ne te sera difficile.
18 Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
Tu fais miséricorde en mille générations, et tu rétribues l'iniquité des pères dans le sein de leurs enfants après eux. Tu es le Dieu grand, le puissant, dont le nom est l'Éternel des armées,
19 manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
Grand en conseil et puissant en exploits; tu as les yeux ouverts sur toutes les voies des enfants des hommes, pour rendre à chacun selon ses voies et selon le fruit de ses œuvres;
20 Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
Tu as fait des signes et des prodiges au pays d'Égypte, jusqu'à ce jour, et en Israël et parmi les hommes, et tu t'es acquis un renom tel qu'il est aujourd'hui.
21 Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
Tu as retiré du pays d'Égypte Israël ton peuple, avec des prodiges et des miracles, à main forte et à bras étendu, et avec une grande terreur.
22 Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
Et tu leur as donné ce pays, que tu avais juré à leurs pères de leur donner, pays où coulent le lait et le miel;
23 Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
Et ils vinrent et en prirent possession. Mais ils n'ont point obéi à ta voix, et n'ont point marché dans ta loi; ils n'ont rien fait de tout ce que tu leur avais commandé de faire. C'est pourquoi tu as fait que tout ce mal leur est arrivé.
24 “Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
Voici, les terrasses s'élèvent contre la ville pour la prendre, et la ville va être livrée entre les mains des Caldéens qui combattent contre elle, et abandonnée à l'épée, à la famine et à la peste. Ce que tu as dit est arrivé, et voici, tu le vois!
25 Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
Et néanmoins, Seigneur Éternel! tu m'as dit: “Achète ce champ à prix d'argent et prends-en des témoins” - Et la ville est livrée entre les mains des Caldéens!
26 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole de l'Éternel fut adressée à Jérémie, en ces termes:
27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
Voici, je suis l'Éternel, le Dieu de toute chair; y a-t-il rien qui me soit difficile?
28 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
C'est pourquoi, ainsi a dit l'Éternel: Voici je vais livrer cette ville entre les mains des Caldéens, entre les mains de Nébucadnetsar, roi de Babylone, qui la prendra.
29 Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
Et les Caldéens qui combattent contre cette ville, vont entrer; ils mettront le feu à cette ville, et ils la brûleront, avec les maisons sur les toits desquelles on a fait des encensements à Baal et des libations à d'autres dieux, pour m'irriter.
30 “Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
Car les enfants d'Israël et les enfants de Juda n'ont fait, dès leur jeunesse, que ce qui est mal à mes yeux; car les enfants d'Israël ne font que m'irriter par les œuvres de leurs mains, dit l'Éternel.
31 Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
Car cette ville m'a été un objet de colère et d'indignation, depuis le jour où on l'a bâtie jusqu'à ce jour, en sorte que je l'ôte de devant ma face;
32 Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
A cause de tout le mal que les enfants d'Israël et les enfants de Juda ont fait pour m'irriter, eux, leurs rois, leurs chefs, leurs sacrificateurs et leurs prophètes, les hommes de Juda et les habitants de Jérusalem.
33 Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
Ils m'ont tourné le dos et non le visage. On les a enseignés, enseignés dès le matin; mais ils n'ont pas été dociles pour recevoir instruction.
34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
Ils ont mis leurs abominations dans la maison sur laquelle est invoqué mon nom, pour la souiller.
35 Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
Et ils ont bâti les hauts lieux de Baal, dans la vallée des fils de Hinnom, pour faire passer leurs fils et leurs filles par le feu à Moloc, ce que je ne leur avais point commandé; et il ne m'était jamais venu à la pensée qu'on fît une telle abomination, pour faire pécher Juda.
36 “Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
Et maintenant, à cause de cela, ainsi a dit l'Éternel, le Dieu d'Israël, touchant cette ville dont vous dites qu'elle va être livrée entre les mains du roi de Babylone, par l'épée, par la famine et par la peste:
37 tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
Voici, je les rassemblerai de tous les pays où je les aurai chassés dans ma colère, dans ma fureur, dans une grande indignation; je les ferai revenir en ce lieu, et y habiter en sûreté.
38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
Alors ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu.
39 Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
Et je leur donnerai un même cœur et un même chemin, afin qu'ils me craignent toujours, pour leur bien et pour celui de leurs enfants après eux.
40 Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
Et je traiterai avec eux une alliance éternelle; je ne me retirerai plus d'eux, je leur ferai du bien, et je mettrai ma crainte dans leurs cœurs, afin qu'ils ne se détournent pas de moi.
41 Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
Et je me réjouirai en leur faisant du bien; et je les planterai véritablement dans ce pays, de tout mon cœur et de toute mon âme.
42 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
Car ainsi a dit l'Éternel: Comme j'ai fait venir tout ce grand mal sur ce peuple, je ferai aussi venir sur eux tout le bien que je leur promets.
43 Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
Et l'on achètera des champs dans ce pays dont vous dites: C'est un désert, sans homme ni bête; il est livré entre les mains des Caldéens.
44 Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
On y achètera des champs à prix d'argent, on en écrira les contrats, et on les cachètera, et on prendra des témoins, dans le pays de Benjamin et aux environs de Jérusalem, dans les villes de Juda, dans les villes de la montagne, dans les villes de la plaine et dans les villes du midi. Car je ferai revenir leurs captifs, dit l'Éternel.