< Irmiya 32 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
La parole qui vint à Jérémie de par l’Éternel, en la dixième année de Sédécias, roi de Juda (ce fut la dix -huitième année de Nebucadretsar).
2 Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
Et l’armée du roi de Babylone assiégeait alors Jérusalem, et Jérémie le prophète était enfermé dans la cour de la prison qui était dans la maison du roi de Juda,
3 Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
où Sédécias, roi de Juda, l’avait enfermé, disant: Pourquoi prophétises-tu, disant: Ainsi dit l’Éternel: Voici, je livre cette ville en la main du roi de Babylone, et il la prendra;
4 Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
et Sédécias, roi de Juda, ne sera pas délivré de la main des Chaldéens, car certainement il sera livré en la main du roi de Babylone, et il lui parlera bouche à bouche, et ses yeux verront ses yeux;
5 Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
et il fera aller Sédécias à Babylone, et il sera là, jusqu’à ce que je le visite, dit l’Éternel: si vous combattez contre les Chaldéens, vous ne réussirez pas?
6 Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et Jérémie dit: La parole de l’Éternel vint à moi, disant:
7 Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
Voici, Hanameël, fils de Shallum ton oncle, vient vers toi, disant: Achète-toi mon champ qui est à Anathoth, car le droit de rachat est à toi pour l’acheter.
8 “Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
Et Hanameël, fils de mon oncle, vint vers moi, selon la parole de l’Éternel, dans la cour de la prison, et me dit: Achète, je te prie, mon champ qui est à Anathoth, dans le pays de Benjamin, car à toi est le droit d’héritage, et à toi le rachat: achète-le pour toi. Et je connus que c’était la parole de l’Éternel.
9 saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
Et j’achetai de Hanameël, fils de mon oncle, le champ qui est à Anathoth; et je lui pesai l’argent, 17 sicles d’argent;
10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
et j’en écrivis la lettre, et je la scellai, et je la fis attester par des témoins, et je pesai l’argent dans la balance;
11 Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
et je pris la lettre d’achat, celle qui était scellée [selon] le commandement et les statuts, et celle qui était ouverte;
12 na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
et je donnai la lettre d’achat à Baruc, fils de Nérija, fils de Makhséïa, sous les yeux de Hanameël [le fils de] mon oncle, et sous les yeux des témoins qui avaient signé à la lettre d’achat, [et] sous les yeux de tous les Juifs qui étaient assis dans la cour de la prison.
13 “A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
Et je commandai sous leurs yeux à Baruc, disant:
14 ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
Ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: Prends ces lettres, cette lettre d’achat, celle qui est scellée, et cette lettre ouverte, et mets-les dans un vase de terre, afin qu’elles se conservent beaucoup de jours.
15 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
Car ainsi dit l’Éternel des armées, le Dieu d’Israël: On achètera encore des maisons, et des champs, et des vignes, dans ce pays.
16 “Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
Et après avoir donné à Baruc, fils de Nérija, la lettre d’achat, je priai l’Éternel, disant:
17 “A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
Ah, Seigneur Éternel! voici, tu as fait les cieux et la terre par ta grande puissance, et par ton bras étendu; aucune chose n’est trop difficile pour toi.
18 Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
Tu uses de bonté envers des milliers [de générations], et tu rétribueras l’iniquité des pères dans le sein de leurs fils après eux, toi, le Dieu grand et fort (l’Éternel des armées est son nom),
19 manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
grand en conseil et abondant en œuvres, dont les yeux sont ouverts sur toutes les voies des fils des hommes, pour rendre à chacun selon ses voies et selon le fruit de ses actions;
20 Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
toi qui as fait des signes et des prodiges jusqu’à ce jour dans le pays d’Égypte, et en Israël, et parmi les hommes, et qui t’es fait un nom tel qu’il est aujourd’hui.
21 Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
Et tu as fait sortir ton peuple Israël du pays d’Égypte, avec des signes et avec des prodiges, et à main forte et à bras étendu, et par une grande frayeur;
22 Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
et tu leur as donné ce pays, que tu avais juré à leurs pères de leur donner, un pays ruisselant de lait et de miel;
23 Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
et ils y sont entrés, et l’ont possédé; mais ils n’ont point écouté ta voix, et n’ont pas marché dans ta loi; et tout ce que tu leur avais commandé de faire ils ne l’ont pas fait, de sorte que tu leur as fait rencontrer tout ce mal.
24 “Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
Voici, les terrasses sont venues jusqu’à la ville, pour la prendre; et la ville est livrée par l’épée, et par la famine, et par la peste, en la main des Chaldéens qui combattent contre elle; et ce que tu as dit est arrivé; et voici, tu le vois!
25 Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
Et toi, Seigneur Éternel! tu m’as dit: Achète-toi le champ à prix d’argent, et fais-le attester par des témoins; … et la ville est livrée en la main des Chaldéens!
26 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à Jérémie, disant:
27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
Voici, je suis l’Éternel, le Dieu de toute chair; quelque chose est-il trop difficile pour moi?
28 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
C’est pourquoi, ainsi dit l’Éternel: Voici, je livre cette ville en la main des Chaldéens, et en la main de Nebucadretsar, roi de Babylone; et il la prendra.
29 Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
Et les Chaldéens qui combattent contre cette ville entreront, et mettront le feu à cette ville, et la brûleront, et les maisons sur les toits desquelles on a brûlé de l’encens à Baal et répandu des libations à d’autres dieux, pour me provoquer à colère.
30 “Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
Car les fils d’Israël et les fils de Juda n’ont fait, dès leur jeunesse, que ce qui est mauvais à mes yeux; car les fils d’Israël n’ont fait que me provoquer par l’œuvre de leurs mains, dit l’Éternel.
31 Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
Car cette ville a été [une provocation] à ma colère et à ma fureur, depuis le jour où ils l’ont bâtie jusqu’à ce jour, afin que je l’ôte de devant ma face,
32 Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
à cause de toute l’iniquité des fils d’Israël et des fils de Juda, qu’ils ont commise pour me provoquer, eux, leurs rois, leurs princes, leurs sacrificateurs, et leurs prophètes, et les hommes de Juda, et les habitants de Jérusalem.
33 Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
Ils m’ont tourné le dos et non la face; et je les ai enseignés, me levant de bonne heure et [les] enseignant, et ils n’ont pas écouté pour recevoir l’instruction;
34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
et ils ont mis leurs abominations dans la maison qui est appelée de mon nom, pour la rendre impure;
35 Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
et ils ont bâti les hauts lieux de Baal, qui sont dans la vallée du fils de Hinnom, pour faire passer [par le feu] leurs fils et leurs filles à Moloc: ce que je ne leur ai point commandé; et il ne m’est point monté au cœur qu’ils fassent cette chose abominable, pour faire pécher Juda.
36 “Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
Et maintenant, à cause de cela, l’Éternel, le Dieu d’Israël, dit ainsi touchant cette ville dont vous dites qu’elle est livrée en la main du roi de Babylone par l’épée, et par la famine, et par la peste:
37 tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
Voici, je les rassemblerai de tous les pays où je les ai chassés dans ma colère, et dans ma fureur, et dans [mon] grand courroux; et je les ferai retourner en ce lieu; et je les ferai habiter en sécurité;
38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
et ils seront mon peuple, et moi je serai leur Dieu;
39 Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
et je leur donnerai un seul cœur, et une seule voie, pour me craindre tous les jours, pour leur bien et [le bien] de leurs fils après eux;
40 Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
et je ferai avec eux une alliance éternelle, que je ne me retirerai point d’auprès d’eux, pour leur faire du bien; et je mettrai ma crainte dans leur cœur, pour qu’ils ne se retirent pas de moi.
41 Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
Et je me réjouirai en eux pour leur faire du bien, et je les planterai dans ce pays, en vérité, de tout mon cœur et de toute mon âme.
42 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
Car ainsi dit l’Éternel: Comme j’ai fait venir sur ce peuple tout ce grand mal, ainsi je ferai venir sur eux tout le bien que j’ai prononcé à leur égard.
43 Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
Et on achètera des champs dans ce pays dont vous dites qu’il est une désolation, de sorte qu’il n’y a ni homme, ni bête; il est livré en la main des Chaldéens.
44 Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
On achètera des champs à prix d’argent, et on en écrira les lettres, et on les scellera, et on les fera attester par des témoins dans le pays de Benjamin, et aux environs de Jérusalem, et dans les villes de Juda, et dans les villes de la montagne, et dans les villes du pays plat, et dans les villes du midi; car je rétablirai leurs captifs, dit l’Éternel.

< Irmiya 32 >