< Irmiya 32 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
The word which came to Jeremiah from Jehovah in the tenth year of Zedekiah, the king of Judah, which was the eighteenth year of Nebuchadnezzar.
2 Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
And at that time the army of the king of Babylon was laying siege to Jerusalem, and Jeremiah the prophet was shut up in the court of the prison, which was in the house of the king of Judah.
3 Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
For Zedekiah, the king of Judah, had shut him up, saying, Wherefore dost thou prophesy, and say, “Thus saith Jehovah: Behold, I am about to give this city into the hand of the king of Babylon, and he shall take it;
4 Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
and Zedekiah, the king of Judah, shall not escape out of the hand of the Chaldaeans, but shall surely be delivered into the hand of the king of Babylon, and he shall speak with him mouth to mouth, and his eyes shall behold his eyes;
5 Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
and he shall lead Zedekiah to Babylon, and there shall he be until I visit him, saith Jehovah; though ye fight with the Chaldaeans, ye shall not prosper?”
6 Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then said Jeremiah, The word of Jehovah came to me, and said:
7 Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
Behold, Hanameel, the son of Shallum, thine uncle, will come to thee, and say, Buy thee my field which is in Anathoth, for thine is the redemption-right to buy it.
8 “Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
And so Hanameel, the son of my uncle, came to me in the court of the prison according to the word of Jehovah, and said to me: Buy, I pray thee, my field, which is in Anathoth, for thine is the right of inheritance and redemption; buy it for thyself! Then I knew that this was the word of Jehovah.
9 saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
I bought, therefore, the field of Hanameel, my uncle's son, in Anathoth, and I paid him the money, seventeen shekels of silver.
10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
And I wrote a deed, and sealed it, and took witnesses thereto, and weighed the silver in the balances.
11 Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
And I took the purchase-deed, that which was sealed according to the law and the statutes, and that which was open,
12 na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
and I gave the purchase-deed to Baruch, the son of Neriah, the son of Maaseiah, in the presence of Hanameel, my uncle's son, and in the presence of the witnesses, who subscribed their names to the purchase-deed, and in the presence of all the Jews who sat in the court of the prison.
13 “A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
And I charged Baruch in their presence, saying,
14 ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
Thus saith Jehovah of hosts, the God of Israel: Take these writings, this sealed purchase-deed, and this open deed, and put them into an earthen vessel, that they may endure a great length of time.
15 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
For thus saith Jehovah of hosts, the God of Israel: Yet again shall houses and fields and vineyards be bought in this land.
16 “Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
And when I had delivered the purchase-deed to Baruch, the son of Neriah, I prayed to Jehovah, saying,
17 “A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
Ah, Lord, Jehovah! Behold, thou hast made the heavens and the earth by thy great power and thy stretched-out arm, and there is nothing too hard for thee.
18 Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
Thou showest kindness to a thousand generations, and recompensest the iniquity of the fathers into the bosom of the children who come after them. The great, the mighty God, Jehovah of hosts is his name,
19 manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
great in counsel and mighty in work; for thine eyes are open upon all the ways of the sons of men, to give every one according to his ways, and according to the fruit of his doings;
20 Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
who hast displayed signs and wonders in the land of Egypt even to this day, and in Israel, and among other men, and hast made thee a name, as at this day;
21 Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
and hast brought forth thy people Israel out of the land of Egypt with signs, and with wonders, and with a strong hand, and with a stretched-out arm, and with great terror,
22 Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
and hast given them this land, which thou didst swear to their fathers to give them, a land flowing with milk and honey;
23 Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
and they have come in and possessed it; but they have not obeyed thy voice, nor walked according to thy law. They have done nothing of all which thou commandedst them to do. Therefore hast thou caused all this evil to come upon them.
24 “Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
Behold, the mounds of the enemy have already come up against the city to take it; and the city is given into the hand of the Chaldaeans, who fight against it by means of the sword, and of the famine, and of the pestilence; and what thou hast spoken is come to pass, and, behold, thou seest it.
25 Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
And yet hast thou said to me, O Lord Jehovah, “Buy thee the field for money, and take witnesses thereto!” when the city is given into the hand of the Chaldaeans.
26 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Then came the word of Jehovah to Jeremiah, saying:
27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
Behold, I, Jehovah, am the God of all flesh. Is there anything too hard for me?
28 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
Therefore thus saith Jehovah: Behold, I will give this city into the hand of the Chaldaeans, and into the hand of Nebuchadnezzar, the king of Babylon, and he shall take it.
29 Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
And the Chaldaeans who fight against this city shall come and set this city on fire, and burn it, with the houses upon whose roofs they have offered incense to Baal, and poured out incense to other gods, to provoke me to anger.
30 “Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
For the children of Israel and the children of Judah have done nothing but evil before me from their youth; yea, the children of Israel have but provoked me to anger with the work of their hands, saith Jehovah.
31 Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
For this city hath been the object of my anger and my fury, from the day when they built it even to this day; that I might remove it from before my face,
32 Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
because of all the wickedness of the children of Israel, and of the children of Judah, which they have committed to provoke me to anger, they, their kings, their princes, their priests, and their prophets, and the men of Judah, and the inhabitants of Jerusalem.
33 Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
For they have turned to me the back, and not the face; though I have taught them, rising up early and teaching them, yet have they not hearkened to receive instruction.
34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
And they have set their abominations in the house which is called by my name, to defile it.
35 Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
And they have built the high places of Baal, which are in the valley of the son of Hinnom, to cause their sons and their daughters to pass through the fire to Moloch, which I commanded them not, neither came it into my mind, that they should practise their abomination, to cause Judah to sin.
36 “Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
Yet now thus saith Jehovah, the God of Israel concerning this city, of which ye say, “It is delivered into the hand of the king of Babylon by the sword, and by the famine, and by the pestilence.”
37 tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
Behold, I will gather them out of all the countries whither I have driven them in my anger and my fury and my great wrath, and I will bring them back to this place, and I will cause them to dwell securely,
38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
and they shall be my people, and I will be their God.
39 Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
And I will give them one heart, and one way, to fear me continually, that it may be well with them, and with their children after them.
40 Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
And I will make an everlasting covenant with them, that I will not turn away from them, nor cease to do them good; for I will put my fear in their hearts, that they shall not depart from me.
41 Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
Yea, I will rejoice over them to do them good, and I will plant them in this land in truth, with my whole heart, and with my whole soul.
42 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
For thus saith Jehovah: As I have brought upon this people all this great evil, so will I bring upon them all the good which I have promised them.
43 Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
And fields shall yet be bought in this land, of which ye say, “It is desolate, without man or beast; it is given into the hand of the Chaldaeans.”
44 Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
Fields shall men buy for money, and subscribe deeds, and seal them, and take witnesses, in the land of Benjamin, and in the places about Jerusalem, and in the cities of Judah, and in the cities of the hill-country, and in the cities of the valley, and in the cities of the south; for I will bring them back from their captivity, saith Jehovah.

< Irmiya 32 >