< Irmiya 32 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
The word that came to Jeremias from the Lord in the tenth year of Sedecias king of Juda: the same is eighteenth year of Nabuchodonosor.
2 Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
At that time the army of the king o Babylon besieged Jerusalem: and Jeremias the prophet was shut up in the court of the prison, which was in the house of the king of Juda.
3 Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
For Sedecias king of Juda had shut him up, saying: Why dost thou prophesy, saying: Thus saith the Lord: Behold I will give this city into the hand of the king of Babylon, and he shall take it?
4 Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
And Sedecias king of Juda shall not escape out of the hand of the Chaldeans: but he shall be delivered into the hands of the king of Babylon: and he shall speak to him mouth to mouth, and his eyes shall see his eyes.
5 Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
And he shall lead Sedecias to Babylon: and he shall be there till I visit him, saith the Lord. But if you will fight against the Chaldeans, you shall have no success.
6 Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And Jeremias said: The word of the Lord came to me, saying:
7 Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
Behold, Hanameel the son of Sellum thy cousin shall come to thee, saying: Buy thee my field, which is in Anathoth, for it is thy right to buy it, being akin.
8 “Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
And Hanameel my uncle’s son cam to me, according to the word of the to the entry of the prison, and said me: Buy my held, which is in in the land of Benjamin: for the right of inheritance is thins, and thou art next of kin to possess it. And I understood this was the word of the Lord.
9 saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
And I bought the held of my uncle’s son, that is in Anathoth: and I weighed him the money, seven staters, and ten pieces of silver.
10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
And I wrote it in a book and sealed it, and took witnesses: and I weighed him the money in the balances.
11 Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
And I took the deed of the purchase that was sealed, and the stipulations, and the ratifications with the seals that were on the outside.
12 na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
And I gave the deed of the purchase to Baruch the son of Neri the son of Maasias in the sight of Hanameel my uncle’s son, in the presence of the witnesses that subscribed the book of the purchase, and before all the Jews that sat in the court of the prison.
13 “A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
And I charged Baruch before them, saying:
14 ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
Thus saith the Lord of hosts the God of Israel: Take these writings, this deed of the purchase that is sealed up, and this deed that is open: and put them in an earthen vessel, that they may continue many days.
15 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
For thus saith the Lord of hosts the God of Israel: Houses, and fields, and vineyards shall be possessed again in this land.
16 “Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
And after I had delivered the deed of purchase to Baruch the son of Neri, I prayed to the Lord, saying:
17 “A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
Alas, alas, alas, O Lord God, behold thou hast made heaven and earth by thy great power, and thy stretched out arm: no word shall be hard to thee:
18 Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
Thou shewest mercy unto thousands, and returnest the iniquity of the fathers into the bosom of their children after them: O most mighty, great, and powerful, the Lord of hosts is thy name.
19 manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
Great in counsel and incomprehensible in thought: whose eyes are open upon all the ways of the children of Adam, to render unto every one according to his ways, and according to the fruit of his devices.
20 Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
Who hast set signs and wonders in the land of Egypt even until this day, and in Israel, and amongst men, and hast made thee a name as at this day.
21 Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
And hast brought forth thy people Israel, out of the land of Egypt with signs, and with wonders, and with a strong hand, and a stretched out arm, and with great terror.
22 Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
And best given them this land which thou didst swear to their fathers, to give them a land flowing with milk and honey.
23 Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
And they came in, and possessed it: but they obeyed not thy voice, and they walked not in thy law: and they did not any of those things that thou didst command them to do, and all these evils are come upon them.
24 “Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
Behold works are built up against the city to take it: and the city is given into the hands of the Chaldeans, who fight against it, by the sword, and the famine, and the pestilence: and what thou hast spoken, is all come to pass, as thou thyself seest.
25 Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
And sayest thou to me, O Lord God: Buy a field for money, and take witnesses, whereas the city is given into the hands of the Chaldeans?
26 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
And the word of the Lord came to Jeremias, saying:
27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
Behold I am the Lord the God of all flesh: shall any thing be hard for me?
28 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
Therefore thus saith the Lord: Behold I will deliver this city into the hands of the Chaldeans, and into the hands of the king of Babylon, and they shall take it.
29 Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
And the Chaldeans that fight against this city, shall come and set it on fire, and burn it, with the houses upon whose roofs they offered sacrifice to Baal, and poured out drink offerings to strange gods, to provoke me to wrath.
30 “Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
For the children of Israel, and the children of Juda, have continually done evil in my eyes from their youth: the children of Israel who even till now provoke me with the work of their hands, saith the Lord.
31 Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
For this city hath been to me a provocation and indignation from the day that they built it, until this day, in which it shall be taken out of my sight.
32 Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
Because of all the evil of the children of Israel, and of the children of Juda, which they have done, provoking me to wrath, they and their kings, their princes, and their priests, and their prophets, the men of Juda, and the inhabitants of Jerusalem.
33 Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
And they have turned their backs to me, and not their faces: when I taught them early in the morning, and instructed them, and they would not hearken to receive instruction.
34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
And they have set their idols in the house, in which my name is called upon, to defile it.
35 Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
And they have built the high places of Baal, which are in the valley of the son of Ennom, to consecrate their sons and their daughters to Moloch: which I commanded them not, neither entered it into my heart, that they should do this abomination, and cause Juda to sin.
36 “Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
And now, therefore, thus saith the Lord the God of Israel to this city, whereof you say that it shall be delivered into the hands of the king of Babylon by the sword, and by famine, and by pestilence:
37 tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
Behold I will gather them together out of all the lands to which I have cast them out in my anger, and in my wrath, and in my great indignation: and I will bring them again into this place, and will cause them to dwell securely.
38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
And they shall be my people, and I will be their God.
39 Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
And I will give them one heart, and one way, that they may fear me all days: and that it may be well with them, and with their children after them.
40 Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
And I will make an everlasting covenant with them, and will not cease to do them good: and I will give my fear in their heart, that they may not revolt from me.
41 Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
And I will rejoice over them, when I shall do them good: and I will plant them in this land in truth, with my whole heart, and with all my soul.
42 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
For thus saith the Lord: As I have brought upon this people all this great evil: so will I bring upon them all the good that I now speak to them.
43 Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
And fields shall be purchased in this land: whereof you say that it is desolate, because there remaineth neither man nor beast, and it is given into the hands of the Chaldeans.
44 Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
Fields shall be bought for money, and deeds shall be written, and sealed, and witnesses shall be taken, in the land of Benjamin, and round about Jerusalem, in the cities of Juda, and in the cities on the mountains, and in the cities of the plains, and in the cities that are towards the south: for I will bring their captivity, saith the Lord.