< Irmiya 32 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji a shekara ta goma ta Zedekiya sarkin Yahuda, wanda ya kasance shekara ta goma sha takwas ta Nebukadnezzar.
Det Ord, som kom til Jeremias fra Herren i Judas Konge Zedekias's tiende Aar; det Aar er Nebukadnezars attende Aar;
2 Sojojin sarkin Babilon a lokacin suna ƙawanya wa Urushalima annabi Irmiya kuwa yana a tsare a sansanin matsara a fadar Yahuda.
— og dengang belejrede Kongen af Babels Hær Jerusalem; men Profeten Jeremias var indelukket i Forgaarden til Fængselet, som var i Judas Konges Hus;
3 Zedekiya sarkin Yahuda fa ya sa shi a kurkuku yana cewa, “Don me kake yin annabci? Ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa cinye ta.
hvor Zedekias, Judas Konge, havde indelukket ham og sagt: Hvorfor spaar du og siger: Saa sagde Herren: Se, jeg giver denne Stad i Kongen af Babels Haand, at han skal indtage den,
4 Zedekiya sarkin Yahuda ba zai kuɓuta daga hannuwan Babiloniyawa ba amma tabbatacce za a ba da shi ga sarkin Babilon, zai kuwa yi masa magana fuska da fuska ya kuma gan shi da idanunsa.
og Zedekias, Judas Konge, skal ikke undkomme fra Kaldæernes Haand; men han skal visselig gives i Kongen af Babels Haand, og hans Mund skal tale med hans Mund, og hans Øjne skulle se hans Øjne;
5 Zai kai Zedekiya Babilon, inda zai zauna har sai ya magance shi, in ji Ubangiji. In ka yi yaƙi da Babiloniyawa, ba za ka yi nasara ba.’”
og han skal føre Zedekias til Babel, og han skal blive der, indtil jeg ser til ham, siger Herren; thi om I end stride imod Kaldæerne, skulle I ikke have Lykke. —
6 Irmiya ya ce, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Og Jeremias sagde: Herrens Ord er kommet til mig saalunde:
7 Hananel ɗan Shallum ɗan’uwan mahaifinka zai zo wurinka ya ce, ‘Saya filina a Anatot, domin a matsayinka na dangi na kurkusa hakkinka ne kuma kai ya wajaba ka saye shi.’
Se, Hanameel, din Farbroder, Sallums Søn, kommer til dig og siger: Køb dig min Ager, som er i Anathoth; thi du har Løsningsretten, at du kan købe den.
8 “Sa’an nan, kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa, sai ga Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina ya zo wurina a sansanin matsara ya ce, ‘Saya filina a Anatot a yankin Benyamin. Da yake hakkinka ne ka fanshe shi ka kuma mallake shi, ka sayo shi wa kanka.’ “Sai na gane cewa wannan maganar Ubangiji ce;
Og Hanameel, min Farbroders Søn, kom til mig efter Herrens Ord til Fængselets Forgaard og sagde til mig: Kære, køb min Ager, som er i Anathoth, i Benjamins Land; thi du har Arveretten, og du har Løsningsretten, køb dig den; da fornam jeg, at det var Herrens Ord.
9 saboda haka sai na saye filin a Anatot daga hannun Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina na kuma auna masa shekel goma sha bakwai na azurfa.
Og jeg købte af Hanameel, min Farbroders Søn, Ageren, som var i Anathoth, og vejede ham Pengene til, sytten Sekel Sølv.
10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna shekel a ma’auni.
Og jeg skrev det i Brevet og forseglede det og tog Vidner dertil og vejede Pengene i Vægtskaalerne:
11 Na ɗauki takardar ciniki, takardar da aka rubuta sharuɗan a ciki, da kuma takardar da ba a liƙe ba,
Og jeg tog Købebrevet, det som var forseglet og indeholdt, hvad der var bestemt og fastsat, og det, som var aabent.
12 na kuma ba wa Baruk ɗan Neriya, ɗan Masehiya, wannan takarda a gaban Hananel yaron ɗan’uwan mahaifina da kuma a gaban shaidun da suka sa hannu a takardan ciniki da kuma a gaban dukan Yahudawan da suke zaune a sansanin matsaran.
Og jeg gav Baruk, en Søn af Neria, som var en Søn af Mahasia, Købebrevet for Hanameels, min Farbroders Søns, Øjne og for de Vidners Øjne, som havde underskrevet Købebrevet, for alle de Jøders Øjne, som sade i Fængselets Forgaard.
13 “A gabansu na yi wa Baruk waɗannan umarnai cewa,
Og jeg befalede Baruk for deres Øjne og sagde:
14 ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka ɗauki waɗannan takardun ciniki, wanda aka liƙe da wanda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tulun yumɓu don kada su lalace.
Saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud: Tag disse Breve, dette Købebrev, baade dette forseglede og dette aabne Brev, og læg dem i et Lerkar, at de maa holde sig mange Dage.
15 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa za a sāke saye gidaje, filaye da gonakin inabi a wannan ƙasa.’
Thi saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud: Endnu skal der købes Huse og Agre og Vingaarde i dette Land.
16 “Bayan na ba da takardun ciniki ga Baruk ɗan Neriya, sai na yi addu’a ga Ubangiji na ce,
Og jeg bad til Herren, efter at jeg havde overgivet Baruk, Nerias Søn, Købebrevet og sagde:
17 “A, Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka mai girma da kuma hannunka mai iko. Ba abin da ya gagare ka.
Ak, Herre, Herre! se, du har skabt Himmelen og Jorden ved din store Kraft og ved din udrakte Arm; der er ingen Ting underlig for dig,
18 Kakan nuna ƙauna ga dubbai amma kakan hukunta’ya’ya saboda laifin ubanninsu a bayansu. Ya mai girma da kuma Allah mai iko, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki,
du, som gør Miskundhed imod tusinde og som betaler Fædrenes Misgerning i deres Børns Barm efter dem, du store, du vældige Gud, hvis Navn er Herren Zebaoth,
19 manufofinka da girma suke, ayyukanka kuma masu girma ne. Idanunka suna a buɗe ga dukan hanyoyin mutane; kakan sāka wa kowa gwargwadon halinsa yadda ya dace.
stor i Raad og mægtig i Gerning; thi dine Øjne ere opladte over alle Menneskens Børns Veje til at give hver efter hans Veje og efter hans Idrætters Frugt!
20 Ka aikata ayyukan banmamaki da kuma al’ajabai a Masar ka kuma ci gaba da su har yă zuwa yau, a Isra’ila da kuma a cikin dukan’yan adam, ka kuma sami sunan da har yanzu yake naka.
Du, som har gjort Tegn og underlige Ting i Ægyptens Land, indtil denne Dag, baade iblandt Israel og iblandt andre Mennesker, og har indlagt dig et Navn, som det er paa denne Dag;
21 Ka fitar da mutanenka Isra’ila daga Masar da alamu da abubuwa banmamaki, ta wurin hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi tare da banrazana mai girma.
og du udførte dit Folk Israel af Ægyptens Land, ved Tegn og ved underlige Ting og ved en stærk Haand og ved en udrakt Arm og ved stor Forfærdelse;
22 Ka ba su wannan ƙasa da ka rantse za ka ba wa kakanni kakanninsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
og du gav dem dette Land, som du tilsvor deres Fædre at ville give dem, et Land, som flyder med Mælk og Honning;
23 Suka shiga suka mallake ta, amma ba su yi maka biyayya ba, ba su kuma bi dokarka ba; ba su yi abin da ka umarce su ba. Saboda haka ka kawo masifa a kansu.
og de kom og toge det i Eje, men de hørte ikke din Røst og vandrede ikke efter din Lov; alt det, som du bød dem at gøre, gjorde de ikke; og du lod al denne Ulykke møde dem.
24 “Duba yadda aka gina mahaurai don a kame birni. Saboda takobi, yunwa da annoba, za a ba da birnin ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye shi da yaƙi. Abin da ka faɗa ya faru, yadda kake gani yanzu.
Se, Belejringsvoldene ere komne ind imod Staden til dens Indtagelse, og Staden er given i Kaldæernes Haand, som stride imod den, ved Sværdet og Hungeren og Pesten; og det, som du har talt, er sket, og se, du ser det.
25 Ko da yake za a ba da birnin ga Babiloniyawa, kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka ce mini, ‘Saye fili da azurfa ka kuma sa a shaida cinikin.’”
Og du, Herre, Herre, har dog sagt til mig: Køb dig Ageren for Penge og tag Vidner derpaa, skønt Staden er given i Kaldæernes Haand.
26 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Og Herrens Ord kom til Jeremias, saa lydende:
27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan’yan adam. Akwai wani abin da ya gagare ni?
Se, jeg er Herren, alt Køds Gud; mon nogen Ting skulde være underlig for mig?
28 Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga Babiloniyawa da kuma ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, wanda zai yaƙe ta.
Derfor, saa siger Herren: Se, jeg giver denne Stad i Kaldæernes Haand og i Nebukadnezar, Kongen af Babels Haand, at han skal indtage den.
29 Babiloniyawan da suke yaƙi da wannan birni za su zo ciki su cinna masa wuta; tare da gidaje inda mutane suka tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙona turare a rufin ɗakuna wa Ba’al suka zub da hadayun sha wa waɗansu alloli.
Og Kaldæerne, som stride imod denne Stad, skulle komme og stikke Ild paa denne Stad og opbrænde den og Husene, paa hvis Tage de gjorde Røgelse for Baal og udøste Drikoffer for andre Guder for at opirre mig.
30 “Mutanen Isra’ila da na Yahuda ba abin da suka yi sai mugunta a gabana daga ƙuruciyarsu; tabbatacce, mutanen Isra’ila ba su yi kome ba sai dai tsokane ni da abin da hannuwansu suka yi, in ji Ubangiji.
Thi Israels Børn og Judas Børn have kun gjort ondt for mine Øjne fra deres Ungdom af; og Israels Børn have kun opirret mig med deres Hænders Gerning, siger Herren.
31 Daga ranar da aka gina ta har zuwa yanzu, wannan birni ta tā da fushina da hasalata da dole a kawar da ita daga gabana.
Thi til Vrede for mig og til Harme for mig har denne Stad været fra den Dag, da de byggede den, og indtil denne Dag, saa at jeg maa skaffe den bort fra mit Ansigt
32 Mutanen Isra’ila da na Yahuda sun tsokane ni ta wurin dukan muguntar da suka aikata su, sarakunansu da fadawansu, firistocinsu da annabawa, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima.
formedelst al Israels Børns og Judas Børns Ondskab, som de øvede for at opirre mig, de, deres Konger, deres Fyrster, deres Præster og deres Profeter, baade Judas Mænd og Jerusalems Indbyggere.
33 Sun juya mini bayansu ba fuskokinsu ba; ko da yake na koyar da su sau da sau, ba su saurara ko bi horo na ba.
Og de vendte Ryggen til mig, og ikke Ansigtet; skønt jeg lærte dem tidligt og ideligt, hørte de dog ikke, saa at de annammede Undervisning.
34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi.
Men de satte deres Vederstyggeligheder i det Hus, som er kaldet efter mit Navn, for at besmitte det.
35 Sun gina masujadai kan tudu wa Ba’al a Kwarin Ben Hinnom don su miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ga Molek, ko da yake ban taɓa umarce su ba, bai kuma zo mini cewa su yi abin banƙyama irin wannan ba ta haka suka sa Yahuda ya yi zunubi.
Og de byggede Baalshøjene, som ere i Ben-Hinnoms Dal, for at ofre deres Sønner og deres Døtre til Molek, hvilket jeg ikke havde befalet dem, og hvilket ikke var kommet mig i Sinde, og for at gøre denne Vederstyggelighed, paa det de maatte faa Juda til at synde.
36 “Kana cewa game da wannan birni, ‘Ta wurin takobi, yunwa da annoba za a ba da shi ga sarkin Babilon’; amma ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa
Og nu siger Herren, Israels Gud, derfor saaledes om denne Stad, om hvilken I sige, at den gives i Kongen af Babels Haand, ved Sværdet og ved Hungeren og ved Pesten:
37 tabbatacce zan tattara su daga dukan ƙasashen da na kore su zuwa cikin fushina da hasalata mai girma; zan komo da su wurin nan in sa su zauna lafiya.
Se, jeg samler dem fra alle Landene, hvorhen jeg fordrev dem i min Vrede og i min Harme og i stor Fortørnelse; og jeg vil føre dem tilbage til dette Sted og lade dem bo tryggelig.
38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.
Og de skulle være mig et Folk, og jeg vil være dem en Gud.
39 Zan ba su zuciya ɗaya da aiki ɗaya, don kullum su ji tsorona domin amfaninsu da kuma amfanin’ya’yansu a bayansu.
Og jeg vil give dem eet Hjerte og een Vej, at de skulle frygte mig alle Dage, for at det maa gaa dem vel og deres Børn efter dem.
40 Zan yi madawwamin alkawari da su. Ba zan taɓa barin aikata musu alheri ba, zan kuma iza su su ji tsorona, don kada su ƙara juya daga gare ni.
Og jeg vil slutte en evig Pagt med dem, at jeg ikke vil drage mig tilbage fra dem, med at gøre dem godt; og jeg vil lægge min Frygt i deres Hjerter, at de ikke skulle vige fra mig.
41 Zan yi farin ciki a yin musu alheri, tabbatacce zan su dasa a wannan ƙasa da dukan zuciyata da dukan raina.
Og jeg vil glæde mig over dem ved at gøre dem godt; og jeg vil plante dem i dette Land i Sandhed, af mit ganske Hjerte og af min ganske Sjæl.
42 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, yadda na kawo dukan wannan masifa a kan wannan mutane, haka zan ba su wadatar da na yi musu alkawari.
Thi saa siger Herren: Ligesom jeg lod al den store Ulykke komme over dette Folk, saaledes vil jeg lade alt det gode komme over dem, som jeg taler over dem.
43 Za a sāke sayi filaye a wannan ƙasa da kuka ce, ‘Kango ce, ba mutane ko dabbobi, gama an ba da ita ga Babiloniyawa.’
Og der skal købes Agre i dette Land, om hvilket I sige: Det er øde, uden Folk og Kvæg, det er givet i Kaldæernes Haand.
44 Za a sayi filaye da azurfa, a kuma sa hannu a takardan ciniki, a liƙe a kuma shaida a yankin Benyamin, a ƙauyukan kewayen Urushalima, a garuruwan Yahuda da kuma a garuruwan ƙasar tudu, na yammancin gindin dutse da na Negeb, domin zan maido da wadatarsu, in ji Ubangiji.”
De skulle købe Agre for Penge og skrive Breve og forsegle dem og tage Vidner derpaa, i Benjamins Land og trindt omkring Jerusalem, og i Judas Stæder og i Stæderne paa Bjerget og i Stæderne i Lavlandet og i Stæderne imod Sønden; thi jeg vil omvende deres Fangenskab, siger Herren.

< Irmiya 32 >