< Irmiya 31 >

1 “A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
In that tyme, seith the Lord, Y schal be God to alle the kynredis of Israel; and thei schulen be in to a puple to me.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
The Lord seith these thingis, The puple that was left of swerd, foond grace in desert; Israel schal go to his reste.
3 Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
Fer the Lord apperide to me, and in euerlastynge charite Y louede thee; therfor Y doynge merci drow thee.
4 Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
And eft Y schal bilde thee, and thou, virgyn Israel, schalt be bildid; yit thou schalt be ourned with thi tympans, and schalt go out in the cumpenye of pleieris.
5 Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
Yit thou schalt plaunte vynes in the hillis of Samarie; men plauntynge schulen plaunte, and til the tyme come, thei schulen not gadere grapis.
6 Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
For whi a dai schal be, wherynne keperis schulen crye in the hil of Samarie, and in the hil of Effraym, Rise ye, and stie we in to Sion, to oure Lord God.
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
For the Lord seith these thingis, Jacob, make ye ful out ioye in gladnesse, and neye ye ayens the heed of hethene men; sowne ye, synge ye, and seie ye, Lord, saue thi puple, the residues of Israel.
8 Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
Lo! Y schal brynge hem fro the loond of the north, and Y schal gadere hem fro the fertheste partis of erthe; among whiche schulen be a blynd man, and crokid, and a womman with childe, and trauelynge of child togidere, a greet cumpeny of hem that schulen turne ayen hidur.
9 Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
Thei schulen come in wepyng, and Y schal brynge hem ayen in merci; and Y schal brynge hem bi the strondis of watris in a riytful weie, thei schulen not spurne therynne; for Y am maad a fadir to Israel, and Effraym is my gendrid sone.
10 “Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
Ye hethene men, here ye the word of the Lord, and telle ye in ylis that ben fer, and seie, He that scateride Israel, schal gadere it, and schal kepe it, as a scheepherde kepith his floc.
11 Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
For the Lord ayenbouyte Jacob, and delyuerede hym fro the hond of the myytiere.
12 Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
And thei schulen come, and herye in the hil of Sion; and thei schulen flowe togidere to the goodis of the Lord, on wheete, wyn, and oile, and on the fruyt of scheep, and of neet; and the soule of hem schal be as a watri gardyn, and thei schulen no more hungre.
13 ’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
Thanne a virgyn schal be glad in a cumpenye, yonge men and elde togidere; and Y schal turne the morenyng of hem in to ioie, and Y schal coumforte hem, and Y schal make hem glad of her sorewe.
14 Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
And Y schal greetli fille the soule of prestis with fatnesse, and my puple schal be fillid with my goodis, seith the Lord.
15 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
The Lord seith these thingis, A vois of weilyng, and of wepyng, and of mourenyng, was herd an hiy; the vois of Rachel biwepynge hir sones, and not willynge to be coumfortid on hem, for thei ben not.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
The Lord seith these thingis, Thi vois reste of wepyng, and thin iyen reste of teeres; for whi mede is to thi werk, seith the Lord; and thei schulen turne ayen fro the lond of the enemy.
17 Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
And hope is to thi laste thingis, seith the Lord, and thi sones schulen turne ayen to her endis.
18 “Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
I heringe herde Effraym passinge ouer; thou chastisidist me, and Y am lerned as a yong oon vntemyd; turne thou me, and Y schal be conuertid, for thou art my Lord God.
19 Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
For aftir that thou conuertidist me, Y dide penaunce; and aftir that thou schewidist to me, Y smoot myn hipe; Y am schent, and Y schamede, for Y suffride the schenschipe of my yongthe.
20 Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
For Effraym is a worschipful sone to me, for he is a delicat child; for sithen Y spak of hym, yit Y schal haue mynde on hym; therfor myn entrails ben disturblid on him, Y doynge merci schal haue merci on hym, seith the Lord.
21 “Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
Ordeyne to thee an hiy totyng place, sette to thee bitternesses; dresse thin herte in to a streiyt weie, in which thou yedist; turne ayen, thou virgyn of Israel, turne ayen to these thi citees.
22 Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
Hou longe, douyter of vnstidfast dwellyng, art thou maad dissolut in delices? for the Lord hath maad a newe thing on erthe, a womman schal cumpasse a man.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
The Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Yit thei schulen seie this word in the lond of Juda, and in the citees therof, whane Y schal turne the caytifte of hem, The Lord blesse thee, thou fairnesse of riytfulnesse, thou hooli hil.
24 Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
And Juda, and alle citees therof schulen dwelle in it togidere, erthetilieris, and thei that dryuen flockis.
25 Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
For Y fillide greetli a feynt soule, and Y haue fillid ech hungri soule.
26 A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
Therfor Y am as reisid fro sleep, and Y siy; and my sleep was swete to me.
27 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
Lo! daies comen, seith the Lord, and Y schal sowe the hous of Israel and the hous of Juda with the seed of men, and with the seed of werk beestis.
28 Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
And as Y wakide on hem, to drawe vp bi the roote, and to distrie, and to scatere, and to leese, and to turmente; so Y schal wake on hem, to bilde, and to plaunte, seith the Lord.
29 “A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
In tho daies thei schulen no more seie, The fadres eeten a sour grape, and the teeth of sones weren astonyed; but ech man schal die in his wickidnesse,
30 A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
ech man that etith a sour grape, hise teeth schulen be astonyed.
31 “Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Lo! daies comen, seith the Lord, and Y schal smyte a newe boond of pees to the hous of Israel, and to the hous of Juda;
32 Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
not bi the couenaunte which Y made with youre fadris, in the dai in which Y took the hond of hem, to lede hem out of the lond of Egipt, the couenaunte which thei made voide; and Y was Lord of hem, seith the Lord.
33 “Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
But this schal be the couenaunte, which Y schal smyte with the hous of Israel aftir tho daies, seith the Lord; Y schal yyue my lawe in the entrails of hem, and Y schal write it in the herte of hem, and Y schal be in to God to hem, and thei schulen be in to a puple to me.
34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
And a man schal no more teche his neiybore, and a man his brother, and seie, Knowe thou the Lord; for alle schulen knowe me, fro the leeste of hem `til to the mooste, seith the Lord; for Y schal be merciful to the wickidnessis of hem, and Y schal no more be myndeful on the synne of hem.
35 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
The Lord seith these thingis, that yyueth the sunne in the liyt of dai, the ordre of the moone and of sterris in the liyt of the niyt, whiche disturblith the see, and the wawis therof sownen, the Lord of oostis is name to hym.
36 “In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
If these lawis failen bifore me, seith the Lord, thanne and the seed of Israel schal faile, that it be not a folk bifore me in alle daies.
37 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
The Lord seith these thingis, If heuenes aboue moun be mesurid, and the foundementis of erthe bynethe be souyt out, and Y schal caste awei al the seed of Israel, for alle thingis whiche thei diden, seith the Lord.
38 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
Lo! daies comen, seith the Lord, and a citee schal be bildid to the Lord, fro the tour of Ananeel `til to the yate of the corner.
39 Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
And it schal go out ouer the reule of mesure, in the siyt therof, on the hil Gareb, and it schal cumpasse Goatha,
40 Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”
and al the valei of careyns, and it schal cumpasse aischis, and al the cuntrei of deth, `til to the stronde of Cedron, and til to the corner of the eest yate of horsis; the hooli thing of the Lord schal not be drawun out, and it schal no more be destried with outen ende.

< Irmiya 31 >