< Irmiya 31 >
1 “A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
“At that time,” a declaration of YHWH, “I am the God of all families of Israel, And they are My people.”
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
Thus said YHWH: “A people remaining from the sword Have found grace in the wilderness When Israel went to find rest.”
3 Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
YHWH has appeared to me from afar, “I have loved you with perpetual love, Therefore I have drawn you [with] kindness.
4 Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
I build you again, And you have been built, O virgin of Israel, You put on your tambourines again, And have gone out in the chorus of the playful.
5 Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
You plant vineyards in mountains of Samaria again, Planters have planted, and made common.
6 Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
For there is a day, Watchmen have cried on Mount Ephraim, Rise, and we go up to Zion, to our God YHWH”;
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
For thus said YHWH: “Sing [with] joy for Jacob, And cry aloud at the head of the nations, Sound, praise, and say, Save, O YHWH, Your people, the remnant of Israel.
8 Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
Behold, I am bringing them in from the north country, And have gathered them from the sides of the earth, Blind and lame [are] among them, Conceiving and travailing one—together, A great assembly—they return here.
9 Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
They come in with weeping, And I bring them with supplications, I cause them to go to streams of waters, In a right way—they do not stumble in it, For I have been a Father to Israel, And Ephraim—he [is] My firstborn.”
10 “Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
Hear a word of YHWH, O nations, And declare among the far off in the islands, and say: He who is scattering Israel gathers him, And has kept His flock as a shepherd,
11 Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
For YHWH has ransomed Jacob, And redeemed him from a hand stronger than he.
12 Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
And they have come in, And have sung in the high place of Zion, And flowed to the goodness of YHWH, For wheat, and for new wine, and for oil, And for the young of the flock and herd, And their soul has been as a watered garden, And they do not add to grieve anymore.
13 ’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
“Then a virgin rejoices in a chorus, Both young men and old men—together, And I have turned their mourning to joy, And have comforted them, And gladdened them above their sorrow,
14 Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
And satisfied the soul of the priests [with] fatness, And My people are satisfied with My goodness,” A declaration of YHWH.
15 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
Thus said YHWH: “A voice is heard in Ramah, Wailing [and] the weeping of bitterness, Rachel is weeping for her sons, She has refused to be comforted for her sons, because they are not.”
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
Thus said YHWH: “Withhold your voice from weeping, and your eyes from tears, For there is a reward for your work,” A declaration of YHWH, “And they have turned back from the land of the enemy.
17 Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
And there is hope for your latter end,” A declaration of YHWH, “And the sons have turned back [to] their border.
18 “Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
I have surely heard Ephraim bemoaning himself, You have disciplined me, And I am disciplined, as a heifer [that is] not taught, Turn me back, and I turn back, For You [are] my God YHWH.
19 Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
For after my turning back I regretted, And after my being instructed I struck on the thigh, I have been ashamed, I have also blushed, For I have borne the reproach of my youth.
20 Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
Is Ephraim a precious son to Me? A child of delights? For since My speaking against him, I still thoroughly remember him, Therefore My bowels have been moved for him, I love him greatly,” A declaration of YHWH.
21 “Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
“Set up signs for yourself, Make heaps for yourself, Set your heart to the highway, the way you went, Turn back, O virgin of Israel, Turn back to these cities of yours.
22 Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
Until when do you withdraw yourself, O backsliding daughter? For YHWH has prepared a new thing in the land, Woman surrounds man.”
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
Thus said YHWH of Hosts, God of Israel: “Still they say this word in the land of Judah, And in its cities, In My turning back [to] their captivity, YHWH blesses you, habitation of righteousness, Mountain of holiness.
24 Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
And farmers have dwelt in Judah, And in all its cities together, And they have journeyed in order.
25 Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
For I have satiated the weary soul, And I have filled every grieved soul.”
26 A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
On this I have awoken, and I behold, and my sleep has been sweet to me.
27 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
“Behold, days are coming,” A declaration of YHWH, “And I have sown the house of Israel, And the house of Judah, With seed of man and seed of beast.
28 Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
And it has been, as I watched over them to pluck up, And to break down, and to throw down, And to destroy, and to afflict; So I watch over them to build, and to plant,” A declaration of YHWH.
29 “A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
“In those days they no longer say: Fathers have eaten unripe fruit, And the sons’ teeth are blunted.
30 A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
But—each dies for his own iniquity, Every man who is eating the unripe fruit, His teeth are blunted.
31 “Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Behold, days are coming,” A declaration of YHWH, “And I have made a new covenant With the house of Israel And with the house of Judah,
32 Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
Not like the covenant that I made with their fathers, In the day of My laying hold on their hand, To bring them out of the land of Egypt, In that they made My covenant void, And I ruled over them,” A declaration of YHWH.
33 “Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
“For this [is] the covenant that I make, With the house of Israel, after those days,” A declaration of YHWH, “I have given My law in their inward part, And I write it on their heart, And I have been their God, And they are My people.
34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
And they do not teach anymore Each his neighbor, and each his brother, Saying, Know YHWH, For they all know Me, from their least to their greatest,” A declaration of YHWH; “For I pardon their iniquity, And I make no more mention of their sin.”
35 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Thus said YHWH, Who is giving the sun for a light by day, The statutes of moon and stars for a light by night, Quieting the sea when its billows roar, YHWH of Hosts [is] His Name:
36 “In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
“If these statutes depart from before Me,” A declaration of YHWH, “Even the seed of Israel ceases From being a nation before Me [for] all the days.”
37 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
Thus said YHWH: “If the heavens above can be measured, And the foundations of earth searched below, Even I kick against all the seed of Israel, For all that they have done,” A declaration of YHWH.
38 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
“Behold, days [are coming],” A declaration of YHWH, “And the city has been built for YHWH, From the Tower of Hananeel to the Corner Gate.
39 Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
And the measuring line has gone out again before it, over the height of Gareb, And it has gone around to Goah.
40 Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”
And all the valley of the carcasses and of the ashes, And all the fields to the Brook of Kidron, To the corner of the Horse Gate eastward, [Are] holy to YHWH, It is not plucked up, Nor is it thrown down anymore for all time!”