< Irmiya 31 >

1 “A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
Til hin tid, lyder det fra Herren, vil jeg være alle Israel slægters Gud, og de skal være mit Folk.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
Så siger HERREN: Folket, der undslap Sværdet, fandt Nåde i Ørkenen, Israel vandred til sin Hvile,
3 Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
i det fjerne åbenbarede HERREN sig for dem: Jeg elsked dig med evig Kærlighed, drog dig derfor i Nåde.
4 Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
Jeg bygger dig atter, du skal bygges, Israels Jomfru, igen skal du smykkes med Håndpauke, gå med i de legendes Dans.
5 Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
Vin skal du atter plante på Samarias Bjerge, plante skal du og høste.
6 Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
Thi en Dag skal Vogterne råbe på Efraims Bjerge: "Kom, lad os drage til Zion, til HERREN vor Gud!"
7 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
Thi så siger HERREN: Fryd jer over Jakob med Glæde, jubl over det første blandt Folkene, kundgør med Lovsang og sig: "HERREN har frelst sit Folk, Israels Rest."
8 Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
Se, jeg bringer dem hid fra Nordens Land, samler dem fraJordens Afkroge; iblandt dem er blinde og lamme, frugtsommelige sammen med fødende, i en stor Forsamling vender de hjem.
9 Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
Se, de kommer med Gråd; mens de ydmygt beder, leder jeg dem; jeg fører dem hen til Vandløb ad en jævn Vej, hvor de ej snubler; thi jeg er Israel en Fader, min førstefødte er Efraim.
10 “Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
Hør HERRENs Ord, I Folk, forkynd på fjerne Strande: Han, som spredte Israel, samler det, vogter det som Hyrden sin Hjord;
11 Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
thi HERREN har udfriet Jakob, genløst det af den stærkeres Hånd.
12 Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
De kommer til Zions bjerg og jubler over HERRENs Fylde, over Kom og Most og Olie og over Lam og Kalve. Deres Sjæl er som en vandrig Have, de skal aldrig vansmægte mer.
13 ’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
Da fryder sig Jomfru i Dans, Yngling og Olding tilsammen. Jeg vender deres Kummer til Fryd, giver Trøst og Glæde efter Sorgen.
14 Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
Jeg kvæger Præsterne med Fedt, mit Folk skal mættes med min Fylde, lyder det fra HERREN.
15 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
Så siger HERREN: En Klagerøst høres i Rama, bitter Gråd, Rakel begræder sine Børn, vil ikke trøstes over sine Børn, fordi de er borte.
16 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
Så siger HERREN: Din Røst skal du holde fra Gråd, dine Øjne fra Tårer, thi derer Løn fordin Møje, lyder det fra HERREN; fra Fjendeland vender de hjem;
17 Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
og der er Håb for din Fremtid, lyder det fra HERREN, Børn vender hjem til deres Land.
18 “Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
Jeg hører grant, hvor Efraim klager: "Du tugted mig, og jeg blev tugtet som en utæmmet Kalv; omvend mig, så bliver jeg omvendt, thi du er HERREN min Gud.
19 Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
Thi nu jeg er omvendt, angrer jeg; nu jeg har besindet mig, slår jeg mig på Hofte; jeg er skamfuld og beskæmmet, thi jeg bærer min Ungdoms Skændsel."
20 Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
Er Efraim min dyrebare Søn, mit Yndlingsbarn? thi så tit jeg taler om ham, må jeg mindes ham kærligt, derfor bruser mit indre, jeg ynkes over ham, lyder det fra HERREN.
21 “Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
Rejs dig Vejvisersten, sæt Mærkesten op, ret din Tanke på Højvejen, Vejen, du gik, vend hjem, du Israels Jomfru, til disse dine Byer!
22 Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
Hvor længe vil du dog tøve, du frafaldne Datter? Thi HERREN skaber nyt i Landet: Kvinde værner om Mand.
23 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
Så siger Hærskarers HERRE, Israels Gud: End skal de i Judas Land og Byer sige dette Ord, når jeg vender deres Skæbne: "HERREN velsigne dig, du Retfærds Bolig, du hellige Bjerg!"
24 Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
Og deri skal Juda bo og alle dets Byer til Hobe, Agerdyrkerne og de omvankende Hyrder.
25 Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
Thi jeg kvæger den trætte Sjæl og mætter hver vansmægtende Sjæl.
26 A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
(Herved vågnede jeg og så mig om, og Søvnen havde været mig sød.)
27 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
Se, Dage skal komme, lyder det fra HERREN, da jeg tilsår Israels Hus og Judas Hus med Sæd at Mennesker og Kvæg.
28 Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
Og som jeg har været årvågen over dem for at oprykke, nedbryde, omstyrte, ødelægge og gøre ilde, således vil jeg være årvågen over dem for at bygge og plante, lyder det fra HERREN.
29 “A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
I hine Dage skal man ikke mere sige: Fædre åd sure Druer, og Børnenes Tænder blev ømme.
30 A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
Nej, enhver skal dø for sin egen Brøde; enhver, der æder sure Druer, får selv ømme Tænder.
31 “Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
Se, Dage skal komme, lyder det fra HERREN, da jeg slutter en ny Pagt med Israels Hus og Judas Hus,
32 Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
ikke som den Pagt jeg sluttede med deres Fædre, dengang jeg tog dem ved Hånden for at føre dem ud af Ægypten, hvilken Pagt de brød, så jeg væmmedes ved dem, lyder det fra HERREN;
33 “Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
nej, dette er den Pagt, jeg efter hine Dage slutter med Israels Hus, lyder det fra HERREN: Jeg giver min Lov i deres Indre og skriver den på deres Hjerter, og jeg vil være deres Gud, og de skal være mit Folk.
34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
Ven skal ikke mere lære sin Ven eller Broder sin Broder og sige: "Kend HERREN!" Thi de skal alle kende mig fra den mindste til den største, lydet det fra HERREN; thi jeg tilgiver deres Brøde og kommer ikke mer deres Synd i Hu.
35 Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Så siger HERREN, han, som satte Solen til at lyse om Dagen og Månen og Stjernerne til at lyse om Natten, han, som oprører Havet, så Bølgerne bruser, han, hvis Navn er Hærskarers HERRE:
36 “In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
Når disse Ordninger viger fra mit Åsyn, lyder det fra HERREN, så skal også Israels Æt for alle Tider ophøre at være et Folk for mit Åsyn.
37 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
Så siger HERREN: Når Himmelen oventil kan udmåles og Jordens Grundvolde nedentil udgranskes, så vil jeg også forkaste Israels Æt for alt, hvad de har gjort, lydet det fra HERREN.
38 “Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
Se, Dage skal komme, lyder det fra HERREN, da Byen skal opbygges for HERREN fra Hananeltårnet til Hjørneporten;
39 Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
og videre skal Målesnoren gå lige ud til Garebs Høj og så svinge mod Goa;
40 Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”
og hele Dalen, Ligene og Asken, og alle Markerne ned til Kedrons Bæk, til Hesteportens Hjørne mod Øst skal være HERREN helliget; det skal aldrig mere oprykkes eller nedlbrydes.

< Irmiya 31 >