< Irmiya 30 >
1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
Слово бывшее ко Иеремии от Господа глаголя:
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
тако рече Господь Бог Израилев глаголя: впиши вся словеса в книги, яже глаголах к тебе.
3 Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
Яко се, дние грядут, рече Господь, и возвращу преселение людий Моих Израиля и Иуды, рече Господь Вседержитель, и возвращу я на землю, юже дах отцем их, и овладеют ею.
4 Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
И сия словеса, яже глагола Господь о Израили и о Иуде.
5 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
Тако рече Господь: глас страха услышите: страх, и несть мира.
6 Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
Вопросите и видите, аще раждает мужеск пол? И о страсе, в немже имети будут чресла и спасение? Понеже видех всякаго человека, и руце его на чреслех его аки раждающия: обратишася лица в желтую болезнь.
7 Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
О, люте! Яко бысть велик день той и несть подобна ему: и время тесно есть Иакову, и от того спасется.
8 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
В той день, рече Господь, сокрушу ярем со выи их и узы их расторгну: и не послужат тии ктому чуждим,
9 A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
но послужат тии Господу Богу своему: и Давида царя их возставлю им.
10 “‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
Сего ради ты не бойся, рабе Мой Иакове, глаголет Господь, ни устрашайся, Израилю: яко се, Аз спасу тя из земли дальния и семя твое из земли пленения их: и возвратится паки Иаков и почиет и всякаго добра исполнен будет, и не будет устрашаяй тя.
11 Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
Яко Аз с тобою есмь, глаголет Господь, спасаяй тя: яко сотворю скончание во всех языцех, в няже разсеях тя: тебе же не сотворю во скончание, но накажу тя в суде и очищая не очищу тя.
12 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
Тако бо глаголет Господь: возставих сокрушение твое, болезненна есть язва твоя,
13 Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
несть судяй суда твоего, на болезнь врачевался еси, пользы несть тебе:
14 Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
вси друзие твои забыша тя, ниже вопросят тя, яже о мире твоем: яко язвою вражиею поразих тя, наказанием твердым: множества ради неправды твоея превозмогоша греси твои.
15 Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
Что вопиеши о сокрушении твоем? Неизцельна есть болезнь твоя множества ради неправды твоея, и твердых ради грехов твоих сотворих ти сия (вся).
16 “‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
Того ради вси ядущии тя изядени будут, и вси врази твои плоть их всю изядят: во множестве неправды твоея умножишася греси твои, сотвориша сия тебе: и будут разграбляющии тя в разграбление, и всех пленяющих тя дам во пленение.
17 Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
Яко обяжу язву твою и от ран твоих уврачую тя, рече Господь: яко расточенным называху тя, Сионе ловитва наша есть, яко несть взыскающаго его.
18 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
Тако глаголет Господь: се, Аз возвращу преселение Иаковле и пленники его помилую, и возградится град в высоту свою, и храм по чину своему утвердится:
19 Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
и изыдут из него поющии и глас играющих, и умножу я, и не умалятся.
20 ’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
И внидут сынове их якоже и прежде, и свидения их пред лицем Моим исправятся: и посещу на вся стужающыя им,
21 Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
и будут крепльшии его на ня, и князь его из него изыдет: и соберу я, и обратятся ко Мне: кто бо есть той, иже приложит сердце свое обратитися ко Мне? Рече Господь.
22 ‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
И будете Ми в люди, и Аз вам буду в Бога.
23 Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
Яко гнев Господень изыде яр, изыде гнев обращаемь, на нечестивыя приидет.
24 Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.
Не отвратится гнев ярости Господни, дондеже сотворит и дондеже исполнит умышление сердца Своего: в последния дни познаете я.