< Irmiya 30 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
The word which came unto Jeremiah, from Yahweh, saying: —
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
Thus, speaketh Yahweh, God of Israel, saying, —Write thee all the words which I have spoken unto thee in a scroll;
3 Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
For lo! days are coming, Declareth Yahweh, when I will turn the captivity of my people Israel and Judah, Saith Yahweh, —and will bring them back into the land which I gave to their fathers that they might possess it.
4 Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
Now, these, are the words which Yahweh hath spoken against Israel and against Judah:
5 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
Yea, thus, saith Yahweh, A voice of trembling, have we heard, Dread and not welfare!
6 Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
Ask, I pray you, and see, whether a male travaileth with child! Why have I seen Every man with his hands upon his loins like a woman in travail, and Every face turned into ghastliness?
7 Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
Alas! for, great, is that day, so that none is like it, —Yea, a time of anguish it is for Jacob, But out of it, shall he be saved.
8 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
And it shall come to pass in that day, Declareth Yahweh of hosts, That I will break his yoke from off thy neck, And thy bonds, will I tear off, —And foreigners shall use him as a slave no more;
9 A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
But they shall serve Yahweh their God, —and David their king, whom I will raise up unto them.
10 “‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
Thou therefore do not fear O my Servant Jacob Urgeth Yahweh, Neither be thou dismayed, O Israel, For behold me! saving thee from afar And thy seed out of the land of their captivity, —Then shall Jacob return, and rest and be quiet, And there shall be none to make him afraid;
11 Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
For with thee, am, I, Declareth Yahweh To save thee, —Though I make an end of all the nations whither I have scattered thee, Yet will I not of thee, make an end, But will chastise thee in measure, not holding thee, guiltless!
12 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
For Thus, saith Yahweh—incurable is thine injury, —Grievous is thy wound:
13 Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
There is none to plead thy cause for binding thee up, —Healing bandages, hast thou none:
14 Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
All thy lovers, have forgotten thee, Thyself, do they not seek, —For With the wounding of an enemy, have I wounded thee With the correction of one who is cruel, Because of the abounding of thine iniquity, Because numerous have been thy sins.
15 Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
Why shouldst thou make outcry over thine injury, Incurable is thy pain? Because of the abounding of thine iniquity, [Because] numerous have been thy sins Have I done these things unto thee.
16 “‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
Therefore, all who devour thee, shall be devoured, And, all thine adversaries—all of them, into captivity, shall depart, —So shall they who plundered thee, be plundered, And all who preyed upon thee, will I deliver up as a prey.
17 Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
For I will put a bandage upon thee, And from thy wounds, will I heal thee Declareth Yahweh, —Because An outcast, they called thee, ‘Tis, Zion! who hath none to ask for her welfare,
18 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
Thus, saith Yahweh—Behold me! bringing back the captivity of the tents of Jacob, And on his habitations, will I have compassion, —So shall the city be built, upon her own mound, And the citadel, upon its own site, shall remain:
19 Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
So shall there proceed from them thanksgiving, and The sound of them who make merry, —And I will multiply them, and they shall not become few, And will make them honourable, and they shall not be despised:
20 ’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
And, his sons, shall come to be as aforetime, And, his assembly, before me, shall continue, —And I will bring punishment on all his oppressors;
21 Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
And, his illustrious one, shall spring, from himself, And his ruler, from his own midst, shall proceed, And I will bring him near and he shall approach unto me, —For who is there that hath pledged his own heart to approach unto me? Demandeth Yahweh:
22 ‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
So shall ye become my people; And, I, will become your God.
23 Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
Lo! the tempest of Yahweh! Indignation, hath come forth, A tempest rolling itself upward, —Upon the head of the lawless ones, shall it hurl itself down!
24 Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.
The fierceness of the anger of Yahweh will not turn back, Until he hath executed nor Until he hath established The purposes of his heart, —In the afterpart of the days, shall ye understand it.

< Irmiya 30 >