< Irmiya 30 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
The word that came to Jeremiah from Jehovah, saying,
2 “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
Thus speaks Jehovah, the God of Israel, saying, Write thee all the words that I have spoken to thee in a book.
3 Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
For, lo, the days come, says Jehovah, that I will turn again the captivity of my people Israel and Judah, says Jehovah, and I will cause them to return to the land that I gave to their fathers, and they shall possess it.
4 Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
And these are the words that Jehovah spoke concerning Israel and concerning Judah.
5 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
For thus says Jehovah: We have heard a voice of trembling, of fear, and not of peace.
6 Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
Ask ye now, and see whether a man travails with child. Why do I see every man with his hands on his loins as a woman in travail, and all faces are turned into paleness?
7 Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
Alas! For that day is great, so that none is like it. It is even the time of Jacob's trouble, but he shall be saved out of it.
8 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
And it shall come to pass in that day, says Jehovah of hosts, that I will break his yoke from off thy neck, and will burst thy bonds. And strangers shall no more make him their bondman,
9 A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
but they shall serve Jehovah their God, and David their king, whom I will raise up to them.
10 “‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
Therefore fear thou not, O Jacob my servant, says Jehovah, nor be dismayed, O Israel. For, lo, I will save thee from afar, and thy seed from the land of their captivity, and Jacob shall return, and shall be quiet and at ease, and none shall make him afraid.
11 Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
For I am with thee, says Jehovah, to save thee. For I will make a full end of all the nations where I have scattered thee, but I will not make a full end of thee. But I will correct thee in measure, and will in no way leave thee unpunished.
12 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
For thus says Jehovah, Thy hurt is incurable, and thy wound grievous.
13 Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
There is none to plead thy cause, that thou may be bound up; thou have no healing medicines.
14 Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
All who love thee have forgotten thee; they seek thee not. For I have wounded thee with the wound of an enemy, with the chastisement of a cruel one, for the greatness of thine iniquity, because thy sins were increased.
15 Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
Why do thou cry for thy hurt? Thy pain is incurable, for the greatness of thine iniquity. Because thy sins were increased, I have done these things to thee.
16 “‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
Therefore all those who devour thee shall be devoured, and all thine adversaries, every one of them, shall go into captivity. And those who despoil thee shall be a spoil, and all who prey upon thee I will give for a prey.
17 Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
For I will restore health to thee, and I will heal thee of thy wounds, says Jehovah, because they have called thee an outcast, saying, It is Zion, whom no man seeks after.
18 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
Thus says Jehovah: Behold, I will turn again the captivity of Jacob's tents, and have compassion on his dwelling-places. And the city shall be built upon its own hill, and the palace shall be inhabited after its own manner.
19 Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
And out of them shall proceed thanksgiving and the voice of those who make merry. And I will multiply them, and they shall not be few. I will also glorify them, and they shall not be small.
20 ’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
Their sons also shall be as formerly, and their congregation shall be established before me. And I will punish all who oppress them.
21 Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
And their prince shall be of themselves, and their ruler shall proceed from the midst of them. And I will cause him to draw near, and he shall approach to me. For who is he who has had boldness to approach to me? says Jehovah.
22 ‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
And ye shall be my people, and I will be your God.
23 Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
Behold, the tempest of Jehovah-wrath-has gone forth, a sweeping tempest. It shall burst upon the head of the wicked.
24 Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.
The fierce anger of Jehovah shall not return until he has executed, and till he has performed the intents of his heart. In the latter days ye shall understand it.

< Irmiya 30 >