< Irmiya 3 >

1 “In mutum ya saki matarsa ta kuwa bar shi ta auri wani mutum, zai iya komo da ita kuma? Ƙasar ba za tă ƙazantu gaba ɗaya ba? Amma kun yi rayuwa kamar karuwa da masoya masu yawa yanzu za ki komo wurina?” In ji Ubangiji.
“Diyelim ki, bir adam karısını boşar, Kadın da onu bırakıp başka biriyle evlenir. Adam bir daha o kadına döner mi? Bu davranış ülkeyi büsbütün kirletmez mi? Oysa sen pek çok oynaşla fahişelik ettin, Yine bana mı dönmek istiyorsun?” diyor RAB.
2 “Ta da idanu ki duba tsaunuka ki gani. Akwai wani wurin da ba a kwana da ke ba? A gefen hanya kin zauna kina jiran masoyanki, kin zauna kamar makiyayi a hamada. Kin ƙazantar da ƙasar da karuwancinki da muguntarki.
“Çıplak tepelere bak da gör. Sevişmediğin yer mi kaldı? Çölde yaşayan bedevi gibi Yol kenarlarında oynaşlarını bekleyip durdun. Fahişeliğinle, kötülüklerinle ülkeyi kirlettin.
3 Saboda haka an hana yayyafi, kuma babu ruwan bazara da ya sauka. Duk da haka kina da irin kallon da karuwa takan yi; kin ƙi ki ji kunya.
Bu yüzden yağmurların ardı kesildi, Son yağmur yağmadı. Yüzsüz bir fahişeye benzedin, Utanç duymak istemedin.
4 Yanzu ba kin kira ni, ‘Mahaifina, abokina daga ƙuruciyata ba,
‘Baba, gençliğimden beri Benim dostumsun’ diye az önce bana seslenmedin mi?
5 kullum za ka riƙa fushi? Hasalarka za tă ci gaba har abada ne?’ Haka kike magana, amma kina aikata dukan muguntar da kika iya yi.”
‘Sonsuza dek kızgın mı kalacaksın? Öfken sonsuza dek mi sürecek?’ Evet, böyle konuşuyor, Ama elinden gelen her kötülüğü yapıyorsun.”
6 A zamanin Sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da marar amincin nan, Isra’ila ta yi? Ta haura kan kowane tudu mai tsayi da kowane gindin itace mai duhuwa ta yi zina a can.
Kral Yoşiya döneminde RAB bana, “Dönek İsrail'in yaptığını gördün mü?” dedi, “Her yüksek tepenin üzerine, her bol yapraklı ağacın altına gidip fahişelik etti.
7 Na yi zaton bayan ta yi wannan duka, za tă komo wurina amma ba tă yi haka ba,’yar’uwarta marar aminci nan Yahuda ta gani.
Bütün bunları yaptıktan sonra bana geri döneceğini düşündüm, ama dönmedi. Hain kızkardeşi Yahuda da gördü bunları.
8 Na ba wa Isra’ila marar bangaskiya takardar saki na kuwa kore ta saboda duk zinanta. Duk da haka na ga cewa’yar’uwarta marar amincin nan Yahuda ba ta da tsoro; ita ma ta fita ta yi zina.
Fahişeliği yüzünden dönek İsrail'i boşayıp ona boşanma belgesini verdiğim halde, kızkardeşi hain Yahuda'nın hiç korkmadığını, gidip fahişelik ettiğini gördüm.
9 Domin fasikancin Isra’ila bai yi tasiri gare ta ba, sai ta ƙazantar da ƙasar ta kuma yi zina da dutse da kuma itace.
Hiç umursamadan fahişeliğiyle ülkeyi kirletti; taşla, ağaçla zina etti.
10 Duk da wannan duka, Yahuda’yar’uwarta rashin amincin ba tă komo gare ni da dukan zuciyarta ba, sai a munafunce,” in ji Ubangiji.
Bütün bunlara karşın, hain kızkardeşi Yahuda içtenlikle değil, göstermelik olarak bana döndü.” Böyle diyor RAB.
11 Ubangiji ya ce mini, “Isra’ila marar bangaskiya ta fi Yahuda marar aminci.
RAB bana, “Dönek İsrail hain Yahuda'dan daha doğru olduğunu gösterdi” dedi,
12 Ka tafi, ka yi shelar saƙon nan wajen arewa cewa, “‘Ki komo, Isra’ila marar bangaskiya,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan ƙara yin fushi da ke ba, gama ni mai jinƙai ne,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan yi fushi da ke har abada ba.
“Git, bu sözleri kuzeye duyur. De ki, “‘Ey dönek İsrail, geri dön’ diyor RAB. ‘Size artık öfkeyle bakmayacağım, Çünkü ben sevecenim’ diyor RAB. ‘Öfkemi sonsuza dek sürdürmem.
13 Ki dai yarda da laifinki kin yi wa Ubangiji Allahnki tawaye, kin watsar da alheranki ga baƙin alloli a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa, ba ki kuwa yi mini biyayya ba,’” in ji Ubangiji.
Ancak suçunu kabul et: Tanrın RAB'be başkaldırdın, Her bol yapraklı ağacın altında Sevgini yabancı ilahlarla paylaştın, Beni dinlemedin.’” Böyle diyor RAB.
14 “Ku komo, ku mutane marasa bangaskiya,” in ji Ubangiji, “gama ni ne mijinku. Zan ɗauke ku, ɗaya daga garuruwanku da kuma biyu daga zuriyarku in kawo ku a Sihiyona.
“Geri dön, ey dönek halk” diyor RAB, “Çünkü kocan benim. Birinizi kentten, ikinizi bir boydan alıp Siyon'a geri getireceğim.
15 Sa’an nan zan ba ku makiyaya da suke yin abin da zuciyata take so, waɗanda za su bishe ku da sani da kuma fahimi.
Size gönlüme göre çobanlar vereceğim; sizi bilgiyle, sağduyuyla güdecekler.
16 A kwanakin, sa’ad da kuka ƙaru sosai a ƙasar,” in ji Ubangiji, “mutane ba za su ƙara yin magana a kan, ‘Akwatin alkawarin Ubangiji ba.’ Ba zai ƙara shiga zuciyarsu ko su tuna ba; ko su bukace shi, ko kuwa su yi wani irinsa ba.
Ülkede büyüyüp sayıca çoğaldığınız günlerde” diyor RAB, “Halk artık, ‘RAB'bin Antlaşma Sandığı’ demeyecek. Sandık bir daha kimsenin aklına gelmeyecek; anımsanmayacak, özlenmeyecek, bir yenisi de yapılmayacak.
17 A lokacin za su ce da Urushalima Kursiyin Ubangiji, kuma dukan al’ummai za su taru a Urushalima don su girmama sunan Ubangiji. Ba za su ƙara bin taurinkai zuciyarsu mai mugunta ba.
O zaman Yeruşalim'e, ‘RAB'bin Tahtı’ diyecekler. RAB'bin adını onurlandırmak için bütün uluslar Yeruşalim'de toplanacak. Bundan böyle kötü yüreklerinin inadı uyarınca davranmayacaklar.
18 A kwanakin gidan Yahuda zai haɗu da gidan Isra’ila, tare kuma za su zo daga ƙasar da take wajen arewa zuwa ƙasar da na ba kakanninsu gādo.
O günlerde Yahuda halkıyla İsrail halkı kuzeyde bir ülkeden birlikte yürüyecek, atalarına mülk olarak vermiş olduğum ülkede bir araya gelecekler.
19 “Ni kaina na faɗa, “‘Da farin ciki zan ɗauke ki kamar’ya’yana maza in ba ki ƙasa mai daɗi, gādo mafi kyau da wata al’umma.’ Na zaci za ki kira ni ‘Mahaifi’ ba za ki ƙara rabuwa da bina ba.
“Ben RAB, demiştim ki, ‘Ne kadar isterdim Seni çocuklarımdan saymayı; Sana güzel ülkeyi, Ulusların en güzel mülkünü vermeyi! Bana baba diyeceğini, Benden hiç ayrılmayacağını düşündüm.
20 Amma kamar mace marar aminci ga mijinta, haka kika kasance marar aminci gare ni, ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji.
Ama bir kadın kocasına nasıl ihanet ederse, Sen de bana öyle ihanet ettin, ey İsrail halkı!’” Böyle diyor RAB.
21 An ji kuka a filayen tuddai, kuka da roƙon mutanen Isra’ila, domin sun lalace hanyoyinsu sun kuma manta da Ubangiji Allahnsu.
Çıplak tepelerde bir ses duyuluyor, İsrail halkının ağlayışı ve yakarışı. Çünkü doğru yoldan saptılar, Tanrıları RAB'bi unuttular.
22 “Ku komo, mutane marasa bangaskiya; zan warkar da ku daga ja da bayanku.” “I, za mu zo wurinka, gama kai ne Ubangiji Allahnmu.
“Geri dönün, ey dönek çocuklar, Dönekliğinizi iyileştireyim.” Halk, “İşte buradayız, sana geliyoruz!” diyor, “Çünkü Tanrımız RAB sensin.
23 Tabbatacce hayaniyar bin gumaka a kan tuddai da duwatsu banza ne; tabbatacce a wurin Ubangiji Allahnmu ne akwai ceton Isra’ila.
Kuşkusuz dağlardan, Tepelerden gelen tapınma sesleri aldatıcıdır. Kuşkusuz İsrail'in kurtuluşu Tanrımız RAB'dedir.
24 Daga ƙuruciyarmu allolin kunya sun cinye mu amfanin wahalar kakanninmu garkunan tumakinsu da na awakinsu, yaransu maza da mata.
Gençliğimizden bu yana Atalarımızın emeğinin ürününü, Davarlarını, sığırlarını, Oğullarını, kızlarını Utanılası putlar yedi.
25 Bari mu kwanta mu sha kunya, bari kuma kunyarmu ta rufe mu. Mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi, da mu da kakanninmu; daga ƙuruciyarmu har yă zuwa yau ba mu yi wa Ubangiji Allahnmu biyayya ba.”
Utanç içinde yatalım, Rezilliğimiz bizi örtsün! Çünkü biz de atalarımız da Gençliğimizden bu yana Tanrımız RAB'be karşı günah işledik, Tanrımız RAB'bin sesine kulak asmadık.”

< Irmiya 3 >