< Irmiya 3 >

1 “In mutum ya saki matarsa ta kuwa bar shi ta auri wani mutum, zai iya komo da ita kuma? Ƙasar ba za tă ƙazantu gaba ɗaya ba? Amma kun yi rayuwa kamar karuwa da masoya masu yawa yanzu za ki komo wurina?” In ji Ubangiji.
On dit: si quelqu'un délaisse sa femme, et qu'elle se séparant de lui se joigne à un autre mari, [le premier mari] retournera-t-il encore vers elle? Le pays même n'en serait-il pas entièrement souillé? Or toi, tu t'es prostituée à plusieurs amoureux, toutefois retourne-toi vers moi, dit l'Eternel.
2 “Ta da idanu ki duba tsaunuka ki gani. Akwai wani wurin da ba a kwana da ke ba? A gefen hanya kin zauna kina jiran masoyanki, kin zauna kamar makiyayi a hamada. Kin ƙazantar da ƙasar da karuwancinki da muguntarki.
Lève tes yeux vers les lieux élevés, et regarde quel est le lieu où tu ne te sois point abandonnée; tu te tenais par les chemins, comme un Arabe au désert; et tu as souillé le pays par tes débauches, et par ta malice.
3 Saboda haka an hana yayyafi, kuma babu ruwan bazara da ya sauka. Duk da haka kina da irin kallon da karuwa takan yi; kin ƙi ki ji kunya.
C'est pourquoi les pluies ont été retenues, et il n'y a point eu de pluie de la dernière saison, et tu as un front de femme débauchée; tu n'as point voulu avoir de honte.
4 Yanzu ba kin kira ni, ‘Mahaifina, abokina daga ƙuruciyata ba,
Ne crieras-tu point désormais vers moi: mon Père, tu es le conducteur de ma jeunesse?
5 kullum za ka riƙa fushi? Hasalarka za tă ci gaba har abada ne?’ Haka kike magana, amma kina aikata dukan muguntar da kika iya yi.”
Tiendra-t-il [sa colère] à toujours, et me la gardera-t-il à jamais? Voici, tu as [ainsi] parlé, et tu as fait ces maux-là, autant que tu as pu.
6 A zamanin Sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da marar amincin nan, Isra’ila ta yi? Ta haura kan kowane tudu mai tsayi da kowane gindin itace mai duhuwa ta yi zina a can.
Aussi l'Eternel me dit aux jours du Roi Josias: n'as-tu point vu ce qu'Israël la revêche a fait? elle s'en est allée sur toute haute montagne, et sous tout arbre vert, et elle s'y est prostituée.
7 Na yi zaton bayan ta yi wannan duka, za tă komo wurina amma ba tă yi haka ba,’yar’uwarta marar aminci nan Yahuda ta gani.
Et quand elle a eu fait toutes ces choses, j'ai dit: retourne-toi vers moi; mais elle n'est point retournée; ce que sa sœur Juda la perfide a vu;
8 Na ba wa Isra’ila marar bangaskiya takardar saki na kuwa kore ta saboda duk zinanta. Duk da haka na ga cewa’yar’uwarta marar amincin nan Yahuda ba ta da tsoro; ita ma ta fita ta yi zina.
Et j'ai vu que pour toutes les occasions par lesquelles Israël la revêche avait commis adultère, je l'ai renvoyée, et lui ai donné ses lettres de divorce; toutefois Juda sa sœur l'infidèle n'a point eu de crainte, mais s'en est allée, et elle aussi s'est prostituée.
9 Domin fasikancin Isra’ila bai yi tasiri gare ta ba, sai ta ƙazantar da ƙasar ta kuma yi zina da dutse da kuma itace.
Et il est arrivé que par la facilité qu'elle a à s'abandonner elle a souillé le pays, et a commis adultère avec la pierre et le bois.
10 Duk da wannan duka, Yahuda’yar’uwarta rashin amincin ba tă komo gare ni da dukan zuciyarta ba, sai a munafunce,” in ji Ubangiji.
Et néanmoins pour tout ceci, Juda sa sœur la perfide n'est point retournée à moi de tout son cœur, mais avec mensonge, dit l'Eternel.
11 Ubangiji ya ce mini, “Isra’ila marar bangaskiya ta fi Yahuda marar aminci.
L'Eternel donc m'a dit: Israël la revêche s'est montrée plus juste que Juda la perfide.
12 Ka tafi, ka yi shelar saƙon nan wajen arewa cewa, “‘Ki komo, Isra’ila marar bangaskiya,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan ƙara yin fushi da ke ba, gama ni mai jinƙai ne,’ in ji Ubangiji, ‘Ba zan yi fushi da ke har abada ba.
Va donc, et crie ces paroles-ci vers l'Aquilon; et dis: retourne-toi, Israël la revêche, dit l'Eternel; je ne ferai point tomber ma colère sur vous; car je suis miséricordieux, dit l'Eternel, et je ne vous la garderai point à toujours.
13 Ki dai yarda da laifinki kin yi wa Ubangiji Allahnki tawaye, kin watsar da alheranki ga baƙin alloli a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa, ba ki kuwa yi mini biyayya ba,’” in ji Ubangiji.
Mais reconnais ton iniquité; car tu as péché contre l'Eternel ton Dieu, et tu t'es prostituée aux étrangers sous tout arbre vert, et n'as point écouté ma voix, dit l'Eternel.
14 “Ku komo, ku mutane marasa bangaskiya,” in ji Ubangiji, “gama ni ne mijinku. Zan ɗauke ku, ɗaya daga garuruwanku da kuma biyu daga zuriyarku in kawo ku a Sihiyona.
Enfants revêches, convertissez-vous, dit l'Eternel; car j'ai droit de mari sur vous; et je vous prendrai l'un d'une ville, et deux d'une lignée, et je vous ferai entrer en Sion.
15 Sa’an nan zan ba ku makiyaya da suke yin abin da zuciyata take so, waɗanda za su bishe ku da sani da kuma fahimi.
Et je vous donnerai des pasteurs selon mon cœur, qui vous paîtront de science et d'intelligence.
16 A kwanakin, sa’ad da kuka ƙaru sosai a ƙasar,” in ji Ubangiji, “mutane ba za su ƙara yin magana a kan, ‘Akwatin alkawarin Ubangiji ba.’ Ba zai ƙara shiga zuciyarsu ko su tuna ba; ko su bukace shi, ko kuwa su yi wani irinsa ba.
Et il arrivera que quand vous serez multipliés et accrus sur la terre, en ces jours-là, dit l'Eternel, on ne dira plus: L'Arche de l'alliance de l'Eternel; elle ne leur montera plus au cœur, ils n'en feront point mention, ils ne la visiteront plus, et cela ne se fera plus.
17 A lokacin za su ce da Urushalima Kursiyin Ubangiji, kuma dukan al’ummai za su taru a Urushalima don su girmama sunan Ubangiji. Ba za su ƙara bin taurinkai zuciyarsu mai mugunta ba.
En ce temps-là on appellera Jérusalem, le Trône de l'Eternel, et toutes les nations s'assembleront vers elle, au Nom de l'Eternel, à Jérusalem, et elles ne marcheront plus après la dureté de leur cœur mauvais.
18 A kwanakin gidan Yahuda zai haɗu da gidan Isra’ila, tare kuma za su zo daga ƙasar da take wajen arewa zuwa ƙasar da na ba kakanninsu gādo.
En ces jours-là la maison de Juda marchera avec la maison d'Israël, et ils viendront ensemble du pays d'Aquilon au pays que j'ai donné en héritage à vos pères.
19 “Ni kaina na faɗa, “‘Da farin ciki zan ɗauke ki kamar’ya’yana maza in ba ki ƙasa mai daɗi, gādo mafi kyau da wata al’umma.’ Na zaci za ki kira ni ‘Mahaifi’ ba za ki ƙara rabuwa da bina ba.
Car j'ai dit: comment te mettrai-je entre [mes] fils, et te donnerai-je la terre désirable, l'héritage de la noblesse des armées des nations? et j'ai dit: tu me crieras, mon Père, et tu ne te détourneras point de moi.
20 Amma kamar mace marar aminci ga mijinta, haka kika kasance marar aminci gare ni, ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji.
Certainement comme une femme pèche contre son ami, ainsi avez-vous péché contre moi, maison d'Israël, dit l'Eternel.
21 An ji kuka a filayen tuddai, kuka da roƙon mutanen Isra’ila, domin sun lalace hanyoyinsu sun kuma manta da Ubangiji Allahnsu.
Une voix a été ouïe sur les lieux élevés, des pleurs de supplications des enfants d'Israël, parce qu'ils ont perverti leur voie, et qu'ils ont mis en oubli l'Eternel, leur Dieu.
22 “Ku komo, mutane marasa bangaskiya; zan warkar da ku daga ja da bayanku.” “I, za mu zo wurinka, gama kai ne Ubangiji Allahnmu.
Enfants rebelles, convertissez-vous, je remédierai à vos rébellions. Voici, nous venons vers toi; car tu [es] l'Eternel notre Dieu.
23 Tabbatacce hayaniyar bin gumaka a kan tuddai da duwatsu banza ne; tabbatacce a wurin Ubangiji Allahnmu ne akwai ceton Isra’ila.
Certainement [on s'attend] en vain aux collines, [et] à la multitude des montagnes; mais c'est en l'Eternel notre Dieu qu'est la délivrance d'Israël.
24 Daga ƙuruciyarmu allolin kunya sun cinye mu amfanin wahalar kakanninmu garkunan tumakinsu da na awakinsu, yaransu maza da mata.
Car la honte a consumé dès notre jeunesse le travail de nos pères, leurs brebis et leurs bœufs, leurs fils et leurs filles.
25 Bari mu kwanta mu sha kunya, bari kuma kunyarmu ta rufe mu. Mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi, da mu da kakanninmu; daga ƙuruciyarmu har yă zuwa yau ba mu yi wa Ubangiji Allahnmu biyayya ba.”
Nous serons gisants dans notre honte, et notre ignominie nous couvrira, parce que nous avons péché contre l'Eternel notre Dieu, nous et nos pères, dès notre jeunesse, et jusqu’à aujourd'hui; et nous n'avons point obéi à la voix de l'Eternel notre Dieu.

< Irmiya 3 >